HotBreaking News
Fetching data...

MAGANI DAGA MANZON ALLAH ﷺ

MAGANI DAGA MANZON ALLAH ﷺ


Yana cikin sunnar Manzon Allah ﷺ neman waraka daga cutuka ta hanya guda ukku;-


1-Hanyar farko

*"Dogaro ga Allah tare da yin Addu'ar neman waraka wadda ta kun shi ayoyin Alqurani mai girma kamar suratul Fatiha ko falaqi da Nasi ko Qulhawa,ko kuma addu'oin neman waraka wanda suka tabbata a sunnar Manzon Allah ﷺ"*


2-Hanya ta biyu;

*"Dogaro ga Allah tare da shan maganin wanda Manzon Allah ﷺ yayi bayanin yana warkar da cuta kaza,kamar shan zuma dan maganin matsalar ciki,ko wani magani da angwada yana maganin cuta"*


Misali:

"Manzon Allah ﷺ yana cewa:

*(Ina uwarninku da shan Nonan saniya,domin nonanta maganine,da kuma kitsenta shima warakane,kuma ku nisanci cin namanta,domin a cikin namanta akwai cuta)*

@الألباني رحمه الله صحيح الجامع الصفحة أو الرقم: 4061


3-Hanya ta Ukku

*"Dogaro ga Allah sannan da aikata wani Ibada wanda sanadiyyarta manzom Allah ﷺ yace ana samun waraqa saboda aikatawa kamar yin sadaka ko gina rijiya"*


Allah ne mafi sani


Allah ka baima dukkan marar sa lafiya daga cikin musulmai lafiya amin.

Load disqus comments

0 Comments

 

Random Posts

3/random/post-list
X

Contact Form

Name

Email *

Message *