*SUNNONIN MANZON ALLAH ﷺ GUDA BIYAR-5 LOKACIN TASHI DAGA BARCI*
*1-Farawa da Ambaton Allah*
Manzon Allah ﷺ ya kasance idan ya tashi daga barci yana cewa;-
*(ﺍﻟﺤﻤﺪ ﻟﻠﻪ ﺍﻟﺬﻱ ﺃﺣﻴﺎﻧﺎ ﺑﻌﺪ ﻣﺎ ﺃﻣﺎﺗﻨﺎ، ﻭﺇﻟﻴﻪ ﺍﻟﻨﺸﻮﺭ*
"ALHAMDU LILLAHIL LAZI AHYANA BA'ADA MAA A MATANA A ILAIKAL NUSHUR"
Manzon Allah ﷺ yana cewa;-
*(Dukkan wanda ya farka cikin dare sai yace:-*
" ﻻ ﺍﻟﻪ ﺇﻻ ﺍﻟﻠﻪ ﻭﺣﺪﻩ ﻻ ﺷﺮﻳﻚ ﻟﻪ ، ﻟﻪ ﺍﻟﻤﻠﻚ ﻭﻟﻪ ﺍﻟﺤﻤﺪ،ﻭﻫﻮ ﻋﻠﻰ ﻛﻞ ﺷﺊ ٍﻗﺪﻳﺮ . ﺍﻟﺤﻤﺪ ﻟﻠﻪ،ﺳﺒﺤﺎﻥ ﺍﻟﻠﻪ،ﻭﻻ ﺍﻟﻪ ﺇﻻ ﺍﻟﻠﻪ،ﻭﺍﻟﻠﻪ ﺃﻛﺒﺮ ﻭﻻ ﺣﻮﻝ ﻭﻻ ﻗﻮﺓ ﺇﻻ ﺑﺎﻟﻠﻪ"
*La ilaha illal-lahu wahdahu la shareeka lah,lahul-mulku walahul-hamd,wahuwa ala kulli shay-in kadeer, subhanal-lah,walhamdu lillah,wala ilaha illal-lah wallahu akbar,wala hawla wala kuwwata illa billahil-aliyyil azeem*Rabbi ghfir li*
Sannan yace;
" ﺍﻟﻠﻬﻢ ﺍﻏﻔﺮ ﻟﻲ "
*(Ko yayi addu'a,za'a amsa masa addu'a,kuma idan yayi alwala yayi Sallah an karbin Sallarsa)*
@ﺍﻟﺒﺨﺎﺭﻱ ( 1154 )
*2-Farawa da yin Aswakin bayan ambaton Allah*.
Manzon Allah ﷺ ya kasance,baya barci face Aswakinsa yana tare da shi,idan ya tashi daga barci sai ya fara da yin Aswaki.
@ﺣﺴﻨﻪ ﺍﻟﻮﺍﺩﻋﻲ ﻓﻲ ﺍﻟﺼﺤﻴﺢ ﺍﻟﻤﺴﻨﺪ - ﺭﻗﻢ : ( 775 ).
*3-Goge alamar barci daga idonsa da hannunsa*.
Acikin wani Hadisi mai tsawo Daga Ibn Abbas ﺭَﺿِﻲَ ﺍﻟﻠَّﻪُ ﻋَﻨْﻬُﻤَﺎ yace;-
*"... Sai Manzon Allah ﷺ ya tashi daga barci,sai ya zauna yana goge alamar barci daga fuskarsa"*
@ﺻﺤﻴﺢ ﺍﻟﺒﺨﺎﺭﻱ - ﺭﻗﻢ : ( 4572 ).
*4-Wanke hannu sau ukku*
Daga Abi Hurairata ﺭَﺿِﻲَ ﺍﻟﻠَّﻪُ ﻋَﻨْﻪُ ,Lallai Manzon Allah ﷺ yace;-
*(Idan dayanku ya tashi daga barcinsa, Kada ya sanya hannunsa acikin mazubi,har sai ya wanke hannunsa sau ukku,domin shi bai san inda hannunsa ya kwana ba)*
️@ﺻﺤﻴﺢ ﻣﺴﻠﻢ - ﺭﻗﻢ : ( 278 )
*5-Shaqa ruwa da facewa sau ukku*
Manzon Allah ﷺ yana cewa;-
*(Idan dayan ku ya tashi daga barci,to ya shaqa ruwa ya face sau Ukku,domin Shaidan yana barci acikin hanncinsa)*
@ﺻﺤﻴﺢ ﻣﺴﻠﻢ - ﺭﻗﻢ:( 238 )
Allah ne mafi sani
*Allah ka bamu ikon koyi da Manzon Allah ﷺ a dukkan rayuwa baki daya*.
0 Comments