HotBreaking News
Fetching data...

YADDA AKE SALLAR GAWA A SAUKAKE

YADDA AKE SALLAR GAWA A SAUKAKE


1-Kabbara ta Farko:

*Idan yayi kabbara ta farko,za'a karanta suratul Fatiha da sura a sirrance.batare da addu'ar bude sallah ba*

@ ﺃﺧﺮﺟﻪ اﻟﺒﺨﺎﺭﻱ (3/ 158) ﻭﺃﺑﻮ ﺩاﻭﺩ (2، 68) ﻭاﻟﻨﺴﺎﺋﻲ (1/ 281) ﻭاﻟﺘﺮﻣﺬﻱ (2/ 142) ﻭاﺑﻦ اﻟﺠﺎﺭﻭﺩ ﻓﻲ " اﻟﻤﻨﺘﻔﻰ " (264) ﻭاﻟﺪاﺭﻗﻄﻨﻲ (191) ﻭاﻟﺤﺎﻛﻢ (1/ 358 - 386)


Kabbara ta biyu 

*2-Sannan yayi kabbara ta biyu,sai yayi Salati ga Annabi Muhammad ﷺ ,satul Ibrahimiyyah*. 

@ﺃﺧﺮﺟﻪ اﻟﺸﺎﻓﻌﻲ ﻓﻲ " اﻻﻡ (1/ 239 - 240) ﻭﻣﻦ ﻃﺮﻳﻘﻪ اﻟﺒﻴﻬﻘﻲ (4/ 39) ﻭاﺑﻦ اﻟﺠﺎﺭﻭﺩ (265) .

Wato shine:

‏«ﺍﻟﻠﻬﻢَّ ﺻﻞِّ ﻋﻠﻰ ﻣﺤﻤَّﺪ ﻭﻋﻠﻰ ﺁﻝ ﻣﺤﻤَّﺪ، ﻛﻤﺎ ﺻﻠﻴﺖَ ﻋﻠﻰ ﺇﺑﺮﺍﻫﻴﻢ ﻭﻋﻠﻰ ﺁﻝ ﺇﺑﺮﺍﻫﻴﻢ؛ ﺇﻧَّﻚ ﺣﻤﻴﺪٌ ﻣﺠﻴﺪ . ﺍﻟﻠﻬﻢَّ ﺑﺎﺭِﻙ ﻋﻠﻰ ﻣﺤﻤَّﺪ ﻭﻋﻠﻰ ﺁﻝ ﻣﺤﻤَّﺪ، ﻛﻤﺎ ﺑﺎﺭﻛﺖَ ﻋﻠﻰ ﺇﺑﺮﺍﻫﻴﻢ ﻭﻋﻠﻰ ﺁﻝ ﺇﺑﺮﺍﻫﻴﻢ؛ ﺇﻧَّﻚ ﺣﻤﻴﺪٌ ﻣﺠﻴﺪ »

*Allahumma salli 'ala Muhammad,wa-'ala ali Muhammad,kama sallayta 'ala Ibraheema wa-'ala ali Ibraheem, innaka Hameedun Majeed, allahumma barik 'ala  Muhammad,wa-'ala ali Muhammad,kama barakta 'ala Ibraheema wa-'ala ali Ibraheem, innaka Hameedun Majeed*. 


Kabbara ta Ukku 

*3-Sannan sai kayi kabbara ta Ukku,Bayan kabbara ta ukku kuma sai kayi addua ga mamacin ka kyautata yimasa addua da jumawa kana yin addua agareshi*

@ﺃﺧﺮﺟﻪ ﺃﺑﻮ ﺩاﻭﺩ (2/ 68) ﻭاﺑﻦ ﻣﺎﺟﻪ (1/ 456) ﻭاﺑﻦ ﺣﺒﺎﻥ ﻓﻲ " ﺻﺤﻴﺤﻪ " ﻭ (754 - ﻣﻮاﺭﺩ) ﻭاﻟﺒﻴﻬﻘﻲ (4/ 40) ﻣﻦ ﺣﺪﻳﺚ ﺃﺑﻲ ﻫﺮﻳﺮﺓ ﻭﺻﺮﺡ اﺑﻦ اﺳﺤﺎﻕ ﺑﺎﻟﺘﺤﺪﻳﺚ ﻋﻨﺪ اﺑﻦ ﺣﺒﺎﻥ.


Ga misalin wasu daga cikin Adduar Manzon Allah ﷺ yayiwa mamaci-

(اﻟﻠﻬﻢ اﻏﻔﺮ ﻟﻪ ﻭاﺭﺣﻤﻪ، ﻭﻋﺎﻓﻪ ﻭاﻋﻒ ﻋﻨﻪ، ﻭﺃﻛﺮﻡ ﻧﺰﻟﻪ، ﻭﻭﺳﻊ ﻣﺪﺧﻠﻪ، ﻭاﻏﺴﻠﻪ ﺑﺎﻟﻤﺎء ﻭاﻟﺜﻠﺞ ﻭاﻟﺒﺮﺩ، ﻭﻧﻘﻪ ﻣﻦ اﻟﺨﻄﺎﻳﺎ ﻛﻤﺎ ﻧﻘﻴﺖ ﻛﻤﺎ ﻳﻨﻘﻲ اﻟﺜﻮﺏ اﻻﺑﻴﺾ ﻣﻦ اﻟﺪﻧﺲ، ﻭﺃﺑﺪﻟﻪ ﺩاﺭا ﺧﻴﺮا ﻣﻦ ﺩاﺭﻩ، ﻭﺃﻫﻼ ﺧﻴﺮا ﻣﻦ ﺃﻫﻠﻪ، ﻭﺯﻭﺟﺎ ﺧﻴﺮا ﻣﻦ ﺯﻭﺟﻪ، ﻭﺃﺩﺧﻠﻪ اﻟﺠﻨﺔ، ﻭﺃﻋﺬﻩ ﻣﻦ ﻋﺬاﺏ اﻟﻘﺒﺮ، ﻭﻣﻦ ﻋﺬاﺏ اﻟﻨﺎﺭ) 

@ﺃﺧﺮﺟﻪ ﻣﺴﻠﻢ (3/ 59 - 60) ﻭاﻟﻨﺴﺎﺋﻲ (1/ 271) ﻭاﺑﻦ ﻣﺎﺟﻪ (1/ 4256) ﻭاﺑﻦ اﻟﺠﺎﺭﻭﺩ (264 - 265) ﻭاﻟﺒﻴﻬﻘﻲ (4/ 40) ﻭاﻟﻄﻴﺎﻟﺴﻲ (999) ﻭﺃﺣﻤﺪ (6/ 23 ﻭ 28) ﻭاﻟﺴﻴﺎﻕ ﻟﻤﺴﻠﻢ،


(اﻟﻠﻬﻢ ﺇﻧﻪ ﻋﺒﺪﻙ ﻭاﺑﻦ ﻋﺒﺪﻙ ﻭاﺑﻦ ﺃﻣﺘﻚ:ﻛﺎﻥ ﻳﺸﻬﺪ ﺃﻥ ﻻ ﺇﻟﻪ ﺃﻻ ﺃﻧﺖ، ﻭﺃﻥ ﻣﺤﻤﺪا ﻋﺒﺪﻙ ﻭﺭﺳﻮﻟﻚ، ﻭﺃﻧﺖ ﺃﻋﻠﻢ ﺑﻪ،اﻟﻠﻬﻢ ﺇﻥ ﻛﺎﻥ ﻣﺤﺴﻨﺎ ﻓﺰﺩ ﻓﻲ ﺣﺴﻨﺎﺗﻪ، ﻭﺇﻥ ﻛﺎﻥ ﻣﺴﻴﺌﺎ ﻓﺘﺠﺎﻭﺯ ﻋﻦ ﺳﻴﺌﺎﺗﻪ، اﻟﻠﻬﻢ ﻻ ﺗﺤﺮﻣﻨﺎ ﺃﺟﺮﺓ، ﻭﻻ ﺗﻔﺘﻨﺎ ﺑﻌﺪﻩ) 

@ﺃﺧﺮﺟﻪ ﻣﺎﻟﻚ (1 - 227) ﻭﻋﻨﻪ ﻣﺤﻤﺪ ﺑﻦ اﻟﺤﺴﻦ (164 - 165) 


Kabbara ta Hudu 

*4-Sannan kayi kabbara ta hudu,bayan kayi kabbara ta hudu sai ka sakeyiwa mamaci addua ko kayiwa sauran muslmai addua.sannan kayi sallama*


Allah ne mafi sani.


NB

Ana daga hannune kadai sau daya ne a cikin sallar gawa, wato lokacin kabbarar Harama,sannan sai mutum ya dora hannunsa na dama akan na hagu abisa kirjinsa.

@Tirmizy da Darul Qadhny da Baihaqy


Mafi yawan mutane munayin asarar rashin sallar ga mamatan mu,yana da kyau a sami jama'a masu yawa sun sallace gawa saboda samun gafarar ga mamacin.


Annabi ﷺ yana cewa:

(Idan aka sami mutane arba'in wadanda basu shirka suka sallaci gawa suna neman citonaa awajan Allah,face Allah ya basu cetonsa).

@Duba littafin Ahkamul Jana'iz na Sheikhu Albany.


Allah ka bamu ikon yawaita yin sallah ga mamatan mu kuma kayi rahama da gafara a garesu baki daya.

Load disqus comments

0 Comments

 

Random Posts

3/random/post-list
X

Contact Form

Name

Email *

Message *