*ZAN IYA BADA KUDI SABODA A DAUKE NI AIKIN GWAMNATI ?*
*Tambaya*
Assalamualaikum, Malam barka da rana, Dan Allah ina da tambaya ne kamar haka: Malam ya halasta mutum ya bada kudi Dan aba shi aikin Gwamnati?
*Amsa*
Wa alaikum assalam, bai halatta ba, saboda irin wannan kudin ana bayar da shi ne saboda daya daga cikin abubuwa guda biyu:
*1*. Ya zamanto mai Neman aikin ya cancanta a dauke shi, sai kudin da ya bayar su zama kyauta ce ga jagororin daukar aikin, hakan kuma haramun ne kamar yadda hadisin Ibnul-lutbiyya wanda Bukhari da Muslim suka rawaito ya tabbatar.
*2*. Ya zama bai cancanta ba, sai kudin da ya bayar su zamo rashawa da kuma hanyar ha'inci da danne hakkin wadanda ya kamata a dauka, ha'inci da danniya kuma haramun ne.
Duk wanda ya kiyaye hakkin Allah, tabbas zai azurta shi ta inda ba ya zato, wanda kuma ya saba masa zai same shi a Madakata.
Allah ne mafi sani.
Amsawa *Dr. Jamilu Zarewa*
0 Comments