HotBreaking News
Fetching data...

IDAN MIJI YA MUTU KAFIN AMARYA TA TARE, YAYA BATUN GADO DA TAKABA?

*_IDAN MIJI YA MUTU KAFIN AMARYA TA TARE, YAYA BATUN GADO DA TAKABA?_*

*Tambaya:*

Assalam pls an daura auren wasu yau ba'a dauko amarya ba sai gobe, amma Allah yayi wa angon rasuwa..tambayata anan wai shin za tayi takaba? Kuma tanada gadonshi?

*Amsa:*

To dan'uwa idan miji ya mutu bayan an daura aure kafin ya tare da amryarsa, ya wajaba amaryarsa ta yi masa takaba, kuma a bata gadonta cikakke, kamar yadda Annabi ﷺ ya yi hukunci da hakan ga Barwa'u 'yar Washik lokacin da mijinta ya mutu kafin su tare a hadisi mai lamba ta: 1145, wanda Tirmizi ya rawaito kuma ya inganta shi.

Allah ne mafi sani.

5\1\2016

Amsawa:-Dr. Jamilu Zarewa.

Load disqus comments

0 Comments

 

Random Posts

3/random/post-list
X

Contact Form

Name

Email *

Message *