*_IDAN MIJI YA MUTU KAFIN AMARYA TA TARE, YAYA BATUN GADO DA TAKABA?_*
*Tambaya:*
Assalam pls an daura auren wasu yau ba'a dauko amarya ba sai gobe, amma Allah yayi wa angon rasuwa..tambayata anan wai shin za tayi takaba? Kuma tanada gadonshi?
*Amsa:*
To dan'uwa idan miji ya mutu bayan an daura aure kafin ya tare da amryarsa, ya wajaba amaryarsa ta yi masa takaba, kuma a bata gadonta cikakke, kamar yadda Annabi ﷺ ya yi hukunci da hakan ga Barwa'u 'yar Washik lokacin da mijinta ya mutu kafin su tare a hadisi mai lamba ta: 1145, wanda Tirmizi ya rawaito kuma ya inganta shi.
Allah ne mafi sani.
5\1\2016
Amsawa:-Dr. Jamilu Zarewa.
0 Comments