HotBreaking News
Fetching data...

IZALA ta kaddamar da taron koyawa Al'umma sana'oin dogaro da kai

IZALA ta kaddamar da taron koyawa Al'umma sana'oin dogaro da kai.

Daga Baffa Maina Hadejia

Kungiyar wa'azin Addinin Islama ta (JIBWIS) reshen jihar jigawa, Ta bude taron koyawa matasa maza da mata sana'oin da zasu dogara da kansu.

Da yake bayani yayin bude taron Shugaban kungiyar na jaha, Malam Abubakar Jibrin Hadejia, yace kungiyar ba iya wa'azi ta tsaya ba, Tana shirya irin wanna taruka domin zakulo matasanmu a koya masu sana'oin da zasu dogara da kansu, Wanda wannan ne na farko da, kungiyar ta fara kuma zataci gaba insha Allah.

Inda ya karkare da, Inda kungiyar taci gaba da irin wanna za'a kawo karshen shaye-shaye daya addabi matasanmu maza da mata.

Shima Shugaban Kwamittin Shirya taron Sheikh Dr. Abdul'qadir Saleh Kazaure yayi bayanin irin sana'oin da za'a koya wadanda suka hada da, GYARAN WAYAR HANNU, SARQA DA DANKUNNE da sauransu, Inda yace zuwa yanzu kowace karamar hukuma a fadin jihar Jigawa ta aiko da wakilanta kuma za'aci gaba da koyar dasu har zuwa kwana biyar din da'aka tsara insha Allah.

Taron yasamu halattar Shugababanin kungiyar a mataki na jaha da kananan hukumomi da sauran jama'a

Allah ya sakawa dukkanin wadanda suka temaka da Alkhairi Amin.

JIBWIS JIGAWA

11/December/2018.

Load disqus comments

0 Comments

 

Random Posts

3/random/post-list
X

Contact Form

Name

Email *

Message *