HotBreaking News
Fetching data...

SHIN YA HALATTA ARNIYA TA YIWA MUSULMA KITSO ?

*SHIN YA HALATTA ARNIYA TA YIWA MUSULMA KITSO ?*

*Tambaya*

Assalamu alaikum, shin ya halatta Arniyya ta yiwa musulma Kitso ?

*Amsa*

Wa'alaikumus salam

Ya halatta macen da ba musulma ba ta yiwa musulma kitso, saboda a zancen mafi inganci, al'aurar mace ga 'yar'uwarta mace, shi ne daga guiwa zuwa cibiya, babu bambanci tsakanin kafira da musulma a cikin haka, domin a zamanin Annabi s.a.w. Yahudawa mata suna shiga gidan Annabi s.a.w., kuma ba'a samu suna yin shiga ta musamman ba idan suka ga za su shigo, saidai in kafirar tana da wani sharri da ake jin tsoro, to wannan mace za ta iya suturta daga ita, sannan kuma mutukar akwai musulma to ita ta fi dacewa ayi hulda da ita .

ALLAH NE MA FI SANI

*Dr. Jamilu Yusuf Zarewa*

Load disqus comments

0 Comments

 

Random Posts

3/random/post-list
X

Contact Form

Name

Email *

Message *