GWARGWADON HALAYENMU GWARGWADON SHUGABANNINMU
Al-Imam Ibnul Qayyim yana bayanin hikimar Allah a cikin halittarsa da gudanarwarsa sai ya ce:
ﻭﺗﺄﻣﻞ ﺣﻜﻤﺘﻪ ﺗﻌﺎﻟﻰ ﻓﻲ ﺃﻥ ﺟﻌﻞ ﻣﻠﻮﻙ ﺍﻟﻌﺒﺎﺩ ﻭﺃﻣﺮﺍﺀﻫﻢ ﻭﻭﻻﺗﻬﻢ ﻣﻦ ﺟﻨﺲ ﺃﻋﻤﺎﻟﻬﻢ، ﺑﻞ ﻛﺄﻥ ﺃﻋﻤﺎﻟﻬﻢ ﻇﻬﺮﺕ ﻓﻲ ﺻﻮﺭ ﻭﻻﺗﻬﻢ ﻭﻣﻠﻮﻛﻬﻢ، ﻓﺈﻥ ﺳﺘﻘﺎﻣﻮﺍ ﺍﺳﺘﻘﺎﻣﺖ ﻣﻠﻮﻛﻬﻢ، ﻭﺇﻥ ﻋﺪﻟﻮﺍ ﻋﺪﻟﺖ ﻋﻠﻴﻬﻢ، ﻭﺇﻥ ﺟﺎﺭﻭﺍ ﺟﺎﺭﺕ ﻣﻠﻮﻛﻬﻢ ﻭﻭﻻﺗﻬﻢ، ﻭﺇﻥ ﻇﻬﺮ ﻓﻴﻬﻢ ﺍﻟﻤﻜﺮ ﻭﺍﻟﺨﺪﻳﻌﺔ ﻓﻮﻻﺗﻬﻢ ﻛﺬﻟﻚ، ﻭﺇﻥ ﻣﻨﻌﻮﺍ ﺣﻘﻮﻕ ﺍﻟﻠﻪ ﻟﺪﻳﻬﻢ ﻭﺑﺨﻠﻮﺍ ﺑﻬﺎ ﻣﻨﻌﺖ ﻣﻠﻮﻛﻬﻢ ﻭﻭﻻﺗﻬﻢ ﻣﺎ ﻟﻬﻢ ﻋﻨﺪﻫﻢ ﻣﻦ ﺍﻟﺤﻖ ﻭﺑﺨﻠﻮﺍ ﺑﻬﺎ ﻋﻠﻴﻬﻢ، ﻭﺇﻥ ﺃﺧﺬﻭﺍ ﻣﻤﻦ ﻳﺴﺘﻀﻌﻔﻮﻧﻪ ﻣﺎ ﻻ ﻳﺴﺘﺤﻘﻮﻧﻪ ﻓﻲ ﻣﻌﺎﻣﻠﺘﻬﻢ ﺃﺧﺬﺕ ﻣﻨﻬﻢ ﺍﻟﻤﻠﻮﻙ ﻣﺎ ﻻ ﻳﺴﺘﺤﻘﻮﻧﻪ، ﻭﺿﺮﺑﺖ ﻋﻠﻴﻬﻢ ﺍﻟﻤﻜﻮﺱ ﻭﺍﻟﻮﻇﺎﺋﻒ، ﻭﻛﻠﻤﺎ ﻳﺴﺘﺨﺮﺟﻮﻧﻪ ﻣﻦ ﺍﻟﻀﻌﻴﻒ ﻳﺴﺘﺨﺮﺟﻪ ﺍﻟﻤﻠﻮﻙ ﻣﻨﻬﻢ ﺑﺎﻟﻘﻮﺓ، ﻓﻌﻤﺎﻟﻬﻢ ﻇﻬﺮﺕ ﻓﻲ ﺻﻮﺭ ﺃﻋﻤﺎﻟﻬﻢ .
ﻭﻟﻴﺲ ﻓﻲ ﺍﻟﺤﻜﻤﺔ ﺍﻹﻟﻬﻴﺔ ﺃﻥ ﻳﻮﻟﻰ ﻋﻠﻰ ﺍﻷﺷﺮﺍﺭ ﺍﻟﻔﺠﺎﺭ ﺇﻻ ﻣﻦ ﻳﻜﻮﻥ ﻣﻦ ﺟﻨﺴﻬﻢ .
ﻭﻟﻤﺎ ﻛﺎﻥ ﺍﻟﺼﺪﺭ ﺍﻷﻭﻝ ﺧﻴﺎﺭ ﺍﻟﻘﺮﻭﻥ ﻭﺃﺑﺮﻫﺎ ﻛﺎﻧﺖ ﻭﻻﺗﻬﻢ ﻛﺬﻟﻚ، ﻓﻠﻤﺎ ﺷﺎﺑﻮﺍ ﺷﺎﺑﺖ ﻟﻬﻢ ﺍﻟﻮﻻﺓ . ﻓﺤﻜﻤﺔ ﺍﻟﻠﻪ ﺗﺄﺑﻰ ﺃﻥ ﻳﻮﻟﻲ ﻋﻠﻴﻨﺎ ﻓﻲ ﻣﺜﻞ ﻫﺬﻩ ﺍﻷﺯﻣﺎﻥ ﻣﺜﻞ ﻣﻌﺎﻭﻳﺔ ﻭﻋﻤﺮ ﺑﻦ ﻋﺒﺪ ﺍﻟﻌﺰﻳﺰ ﻓﻀﻼ ﻋﻦ ﻣﺜﻞ ﺃﺑﻲ ﺑﻜﺮ ﻭﻋﻤﺮ، ﺑﻞ ﻭﻻﺗﻨﺎ ﻋﻠﻰ ﻗﺪﺭﻧﺎ ﻭﻭﻻﺓ ﻣﻦ ﻗﺒﻠﻨﺎ ﻋﻠﻰ ﻗﺪﺭﻫﻢ، ﻭﻛﻞ ﻣﻦ ﺍﻷﻣﺮﻳﻦ ﻣﻮﺟﺐ ﺍﻟﺤﻜﻤﺔ ﻭﻣﻘﺘﻀﺎﻫﺎ
ﻣﻔﺘﺎﺡ ﺩﺍﺭ ﺍﻟﺴﻌﺎﺩﺓ ﻭﻣﻨﺸﻮﺭ ﻭﻻﻳﺔ ﺍﻟﻌﻠﻢ ﻭﺍﻹﺭﺍﺩﺓ ( /1 253 - 254 )
"Ka lura da hikimar Allah Madaukaki ta sanya Shugabannin talakawa da Sarakunansu da Gomnoninsu gwargwadon halayen talakawan. Kai, kamar ka ce: aiyukan talakawa suna bayyana ne a kamannin Shugabanni da Gomnonin nasu. Idan talakawan sun tsayu a kan Addini sai Shugabannin su tsayu a kan dadai. In talakawan sun zama masu adalci a tsakaninsu sai shugabannin su yi musu adalci a cikin mulkinsu, in talakawan sun zama masu zalunci a tsakaninsu sai Shugabanni da Gomnonin nasu su zama masu zalunci. In makirci da yaudara sun bayyana daga talakawan sai shugabannin ma su zama haka. In talakawan sun ki bayar da hakkokin Allah da yake kansu (kamar Zakka da Sadaka) suka yi rowansu sai Shugabanni da Gomnonin nasu su hana su nasu hakkokin, kuma za su yi rowansu gare su. In talakawan suka yi kwacen abin da ba su cancanta ba daga masu rauni a cikinsu a cikin mu'amalolinsu, sai shugabannin nasu su kwace musu abin da shugabannin ba su cancance shi ba, su dora musu haraji (tax) da aiyukan bautar kasa. Dukkan abin da talakawan za su karba daga masu rauni daga cikinsu haka shugabannin za su karba da karfi daga wajen talakawan. Gomnonin talakawan sun bayyana ne bisa kamannin aiyukan talakawan.
Ba ya daga cikin hikimar Allah ya dora shugabanni ga mutanen banza fajirai face irinsu.
Yayin da farkon Muslunci suka kasance mafiya alherin al'umma mafi biyayya ga Allah sai shugabanninsu suka kasance irinsu. Amma yayin da suka jirkice sai shugabannin suka jirkice tare da su. Saboda haka hikimar Allah ta ki yarda shugabanni irin su Mu'awiya (ra) da Umar bn Abdil'Azeez (r) su zama shugabanninmu a wannan zamani, balle kuma irinsu Abubakar (ra) da Umar (ra)!
Kai, shugabanninmu za su kasance ne gwargwadon yadda muke. Haka shugabannin magabatanmu sun kasance ne gwargwadon yadda magabatan suke, duka wadannan nau'uka biyu shi ne abin da hikimar Allah take hukuntawa".
Da ma Allah ya ce:
{ ﺇِﻥَّ ﺍﻟﻠَّﻪَ ﻟَﺎ ﻳُﻐَﻴِّﺮُ ﻣَﺎ ﺑِﻘَﻮْﻡٍ ﺣَﺘَّﻰ ﻳُﻐَﻴِّﺮُﻭﺍ ﻣَﺎ ﺑِﺄَﻧْﻔُﺴِﻬِﻢْ { [ ﺍﻟﺮﻋﺪ : 11 ]
"Allah ba ya canza abin da ya samu mutane (na bala'i) har sai sun gyara abin da ke tare da su (na laifuka)".
In muna so shugabanninmu su zama masu adalci to mu ma mu zama masu adalci a tsakaninmu!
In muna so shugabanninmu su zama masu gaskiya da rikon amana to mu ma mu zama haka a cikin mu'amalolinmu na yau da kullum!
In muna so shugabanninmu su zama masu tausayin talakawa to mu ma mu zama masu tausayin raunananmu!
In muna so shugabanninmu su zama masu kyautata talakawa to mu ma mu kyautata wa junanmu!
Sai mun gyara kafin Allah ya canza mana.
Rubutawa: Dr. Aliyu Muhd Sani.
Al-Imam Ibnul Qayyim yana bayanin hikimar Allah a cikin halittarsa da gudanarwarsa sai ya ce:
ﻭﺗﺄﻣﻞ ﺣﻜﻤﺘﻪ ﺗﻌﺎﻟﻰ ﻓﻲ ﺃﻥ ﺟﻌﻞ ﻣﻠﻮﻙ ﺍﻟﻌﺒﺎﺩ ﻭﺃﻣﺮﺍﺀﻫﻢ ﻭﻭﻻﺗﻬﻢ ﻣﻦ ﺟﻨﺲ ﺃﻋﻤﺎﻟﻬﻢ، ﺑﻞ ﻛﺄﻥ ﺃﻋﻤﺎﻟﻬﻢ ﻇﻬﺮﺕ ﻓﻲ ﺻﻮﺭ ﻭﻻﺗﻬﻢ ﻭﻣﻠﻮﻛﻬﻢ، ﻓﺈﻥ ﺳﺘﻘﺎﻣﻮﺍ ﺍﺳﺘﻘﺎﻣﺖ ﻣﻠﻮﻛﻬﻢ، ﻭﺇﻥ ﻋﺪﻟﻮﺍ ﻋﺪﻟﺖ ﻋﻠﻴﻬﻢ، ﻭﺇﻥ ﺟﺎﺭﻭﺍ ﺟﺎﺭﺕ ﻣﻠﻮﻛﻬﻢ ﻭﻭﻻﺗﻬﻢ، ﻭﺇﻥ ﻇﻬﺮ ﻓﻴﻬﻢ ﺍﻟﻤﻜﺮ ﻭﺍﻟﺨﺪﻳﻌﺔ ﻓﻮﻻﺗﻬﻢ ﻛﺬﻟﻚ، ﻭﺇﻥ ﻣﻨﻌﻮﺍ ﺣﻘﻮﻕ ﺍﻟﻠﻪ ﻟﺪﻳﻬﻢ ﻭﺑﺨﻠﻮﺍ ﺑﻬﺎ ﻣﻨﻌﺖ ﻣﻠﻮﻛﻬﻢ ﻭﻭﻻﺗﻬﻢ ﻣﺎ ﻟﻬﻢ ﻋﻨﺪﻫﻢ ﻣﻦ ﺍﻟﺤﻖ ﻭﺑﺨﻠﻮﺍ ﺑﻬﺎ ﻋﻠﻴﻬﻢ، ﻭﺇﻥ ﺃﺧﺬﻭﺍ ﻣﻤﻦ ﻳﺴﺘﻀﻌﻔﻮﻧﻪ ﻣﺎ ﻻ ﻳﺴﺘﺤﻘﻮﻧﻪ ﻓﻲ ﻣﻌﺎﻣﻠﺘﻬﻢ ﺃﺧﺬﺕ ﻣﻨﻬﻢ ﺍﻟﻤﻠﻮﻙ ﻣﺎ ﻻ ﻳﺴﺘﺤﻘﻮﻧﻪ، ﻭﺿﺮﺑﺖ ﻋﻠﻴﻬﻢ ﺍﻟﻤﻜﻮﺱ ﻭﺍﻟﻮﻇﺎﺋﻒ، ﻭﻛﻠﻤﺎ ﻳﺴﺘﺨﺮﺟﻮﻧﻪ ﻣﻦ ﺍﻟﻀﻌﻴﻒ ﻳﺴﺘﺨﺮﺟﻪ ﺍﻟﻤﻠﻮﻙ ﻣﻨﻬﻢ ﺑﺎﻟﻘﻮﺓ، ﻓﻌﻤﺎﻟﻬﻢ ﻇﻬﺮﺕ ﻓﻲ ﺻﻮﺭ ﺃﻋﻤﺎﻟﻬﻢ .
ﻭﻟﻴﺲ ﻓﻲ ﺍﻟﺤﻜﻤﺔ ﺍﻹﻟﻬﻴﺔ ﺃﻥ ﻳﻮﻟﻰ ﻋﻠﻰ ﺍﻷﺷﺮﺍﺭ ﺍﻟﻔﺠﺎﺭ ﺇﻻ ﻣﻦ ﻳﻜﻮﻥ ﻣﻦ ﺟﻨﺴﻬﻢ .
ﻭﻟﻤﺎ ﻛﺎﻥ ﺍﻟﺼﺪﺭ ﺍﻷﻭﻝ ﺧﻴﺎﺭ ﺍﻟﻘﺮﻭﻥ ﻭﺃﺑﺮﻫﺎ ﻛﺎﻧﺖ ﻭﻻﺗﻬﻢ ﻛﺬﻟﻚ، ﻓﻠﻤﺎ ﺷﺎﺑﻮﺍ ﺷﺎﺑﺖ ﻟﻬﻢ ﺍﻟﻮﻻﺓ . ﻓﺤﻜﻤﺔ ﺍﻟﻠﻪ ﺗﺄﺑﻰ ﺃﻥ ﻳﻮﻟﻲ ﻋﻠﻴﻨﺎ ﻓﻲ ﻣﺜﻞ ﻫﺬﻩ ﺍﻷﺯﻣﺎﻥ ﻣﺜﻞ ﻣﻌﺎﻭﻳﺔ ﻭﻋﻤﺮ ﺑﻦ ﻋﺒﺪ ﺍﻟﻌﺰﻳﺰ ﻓﻀﻼ ﻋﻦ ﻣﺜﻞ ﺃﺑﻲ ﺑﻜﺮ ﻭﻋﻤﺮ، ﺑﻞ ﻭﻻﺗﻨﺎ ﻋﻠﻰ ﻗﺪﺭﻧﺎ ﻭﻭﻻﺓ ﻣﻦ ﻗﺒﻠﻨﺎ ﻋﻠﻰ ﻗﺪﺭﻫﻢ، ﻭﻛﻞ ﻣﻦ ﺍﻷﻣﺮﻳﻦ ﻣﻮﺟﺐ ﺍﻟﺤﻜﻤﺔ ﻭﻣﻘﺘﻀﺎﻫﺎ
ﻣﻔﺘﺎﺡ ﺩﺍﺭ ﺍﻟﺴﻌﺎﺩﺓ ﻭﻣﻨﺸﻮﺭ ﻭﻻﻳﺔ ﺍﻟﻌﻠﻢ ﻭﺍﻹﺭﺍﺩﺓ ( /1 253 - 254 )
"Ka lura da hikimar Allah Madaukaki ta sanya Shugabannin talakawa da Sarakunansu da Gomnoninsu gwargwadon halayen talakawan. Kai, kamar ka ce: aiyukan talakawa suna bayyana ne a kamannin Shugabanni da Gomnonin nasu. Idan talakawan sun tsayu a kan Addini sai Shugabannin su tsayu a kan dadai. In talakawan sun zama masu adalci a tsakaninsu sai shugabannin su yi musu adalci a cikin mulkinsu, in talakawan sun zama masu zalunci a tsakaninsu sai Shugabanni da Gomnonin nasu su zama masu zalunci. In makirci da yaudara sun bayyana daga talakawan sai shugabannin ma su zama haka. In talakawan sun ki bayar da hakkokin Allah da yake kansu (kamar Zakka da Sadaka) suka yi rowansu sai Shugabanni da Gomnonin nasu su hana su nasu hakkokin, kuma za su yi rowansu gare su. In talakawan suka yi kwacen abin da ba su cancanta ba daga masu rauni a cikinsu a cikin mu'amalolinsu, sai shugabannin nasu su kwace musu abin da shugabannin ba su cancance shi ba, su dora musu haraji (tax) da aiyukan bautar kasa. Dukkan abin da talakawan za su karba daga masu rauni daga cikinsu haka shugabannin za su karba da karfi daga wajen talakawan. Gomnonin talakawan sun bayyana ne bisa kamannin aiyukan talakawan.
Ba ya daga cikin hikimar Allah ya dora shugabanni ga mutanen banza fajirai face irinsu.
Yayin da farkon Muslunci suka kasance mafiya alherin al'umma mafi biyayya ga Allah sai shugabanninsu suka kasance irinsu. Amma yayin da suka jirkice sai shugabannin suka jirkice tare da su. Saboda haka hikimar Allah ta ki yarda shugabanni irin su Mu'awiya (ra) da Umar bn Abdil'Azeez (r) su zama shugabanninmu a wannan zamani, balle kuma irinsu Abubakar (ra) da Umar (ra)!
Kai, shugabanninmu za su kasance ne gwargwadon yadda muke. Haka shugabannin magabatanmu sun kasance ne gwargwadon yadda magabatan suke, duka wadannan nau'uka biyu shi ne abin da hikimar Allah take hukuntawa".
Da ma Allah ya ce:
{ ﺇِﻥَّ ﺍﻟﻠَّﻪَ ﻟَﺎ ﻳُﻐَﻴِّﺮُ ﻣَﺎ ﺑِﻘَﻮْﻡٍ ﺣَﺘَّﻰ ﻳُﻐَﻴِّﺮُﻭﺍ ﻣَﺎ ﺑِﺄَﻧْﻔُﺴِﻬِﻢْ { [ ﺍﻟﺮﻋﺪ : 11 ]
"Allah ba ya canza abin da ya samu mutane (na bala'i) har sai sun gyara abin da ke tare da su (na laifuka)".
In muna so shugabanninmu su zama masu adalci to mu ma mu zama masu adalci a tsakaninmu!
In muna so shugabanninmu su zama masu gaskiya da rikon amana to mu ma mu zama haka a cikin mu'amalolinmu na yau da kullum!
In muna so shugabanninmu su zama masu tausayin talakawa to mu ma mu zama masu tausayin raunananmu!
In muna so shugabanninmu su zama masu kyautata talakawa to mu ma mu kyautata wa junanmu!
Sai mun gyara kafin Allah ya canza mana.
Rubutawa: Dr. Aliyu Muhd Sani.
0 Comments