HotBreaking News
Fetching data...

SUNNONI GUDA BIYAR A LOKACIN KIRAN SALLAH

*_SUNNONI GUDA BIYAR A LOKACIN KIRAN SALLAH_*

Mai gaskiya Yar' mai Gaskiya Nana Aisha Matar Annabi s.a.w Allah ya kara mata yarda tana cewa:
*"Yana cikin babbar Asara mutum yaji Ladan yana kiran Sallah,amma bai bi amsawa mai kiran Sallarba"*.

Ibn Qaiyim Allah yayi masa Rahama yana cewa:
*"Akwai sunnoni guda biyar tabbatattu lokacin kiran Sallah"*.

1-SUNNA TA FARKO-(1).
*"Amsawa mai kiran Sallah wato ka riqa fadar abinda mai kiran Sallah yake fada lokacin kiran Sallah"*.

DALILI AKAN HAKA
Fadar Annabi s.a.w:
(Idan Ladan yace
"الله أكبر الله أكبر".
ALLAHU AKBAR ALLAHU AKBAR,sai dayanku yace:الله أكبر الله أكبر".
ALLAHU AKBAR ALLAHU AKBAR,sannan idan Ladan yace:
"أشهد أن لا إله إلا الله"
"ASH'HADU AN LAA ILAHA ILLALLAH",sai yace
أشهد أن لا إله إلا الله"
"ASH'HADU AN LAA ILAHA ILLALLAH",idan ladan yace:
"أشهد أن محمدا رسول الله"
"ASH'HADU ANNA MUHAMMADAR RASULILLAH" Sai yace:
"أشهد أن محمدا رسول الله"
"ASH'HADU ANNA MUHAMMADAR RASULILLAH" idan Ladan yace:
"حي على الصلاة"
"HAYYA ALAS SALLAH" sai yace:
"لاحول ولا قوة إلا بالله"
"LAA HAULA WALA QUWWATA ILLA BILLAH",idan yace:
"حي على الفلاح"
"HAYYA ALAL FALAH" sai yace
لاحول ولا قوة إلا بالله"
_"LAA HAULA WALA QUWWATA ILLA BILLAH"_
 idan yace:
"الله أكبر الله أكبر".
ALLAHU AKBAR ALLAHU AKBAR,sai dayanku yace:الله أكبر الله أكبر".
ALLAHU AKBAR ALLAHU AKBAR,idan yace:
لا إله إلا الله"
"LAA ILAHA ILLALLAH",sai yace
لا إله إلا الله"
"LAA ILAHA ILLALLAH" wanda yace LAA ILAHA ILLALLAH" azuciyarsa ya shiga aljanna).
@رواه مسلم .

2-SUNNA TA BIYU-(2)
*"Yin Salati ga Annbi s.a.w bayan kare kiran Sallah"*.

DALILI AKAN HAKAN.
Manzon Allah s.a.w yana cewa:
*(idan Dayanku yaji kiran Sallah to yafadi irin abinda mai kiran Sallah yake fada,sannan yayi Salati agareni,domin wanda yayi min salati guda daya Allah zai yi masa guda goma)*.
@رواه مسلم.

3-SUNNATA TA UKKU-(3)
*"Roqawa Annabi s.a.w WASIILA a wajan Allah ta hanyar karanta adduar da Annabi s.a.w ya koyar dan roqa masa WASIILA"*

DALILI AKAN HAKA
Annabi s. a.w yana cewa:
*(idan Dayanku yaji kiran Sallah to yafadi irin abinda mai kiran Sallah yake fada,sannan yayi Salati agareni,domin wanda yayi min salati guda daya Allah zai yi masa guda goma, Sannan ya roqa min WASIILA domin ita wani matsayine acikin aljanna,bata dacewa da kowa sai ga wani bawa daga cikin bayin Allah kuma ina Sa ran nine mai wannan matsayi Dukkan wanda ya roqa min wannan matsayin to cetona ya tabbata agareshi)*.
@رواه مسلم .

ADDUAR ROQAWA ANNABI S.A.W :-
(اللهم رب هذه الدعوة التامة ، والصلاة القائمة . آت محمدا الوسيلة ، والفضيلة ، وابعثه مقاما محمودا الذي وعدته)
*Wanda ya karanta bayan kiran Sallah citon Annabi s.a.w ya Tabbata agareshi ranar alqiyama)*.
@Muslim.

4-SUNNA TA HUDU-(4)
"Fadar:
"رضيت بالله ربا وبالإسلام دينا وبمحمد صل الله عليه وسلم رسولا ".
*"RADHEETU BILLAHI RABBAN WABIL ISLAMU DINAN WABI MUHAMMAD S.A.W RASULAN"*

DALILI AKAN HAKA
Manzon Allah s.a.w yace:
'(Wanda ya fada alokacin da yagama jin mai kiran Sallah:-*
(وأنا أشهد أن لا إله إلا الله وحده لا شريك له ، وأن محمدا عبده ورسوله . رضيت بالله ربا ، وبالإسلام دينا ، وبمحمد صل الله عليه وسلم رسولا).
*Wanda ya fadin wannann Allah ya gafarta masa zunubansa)*.
@رواه مسلم .

5-SUNNA TA BIYAR-(5)
"Mutum ya roqawa kansa Abinda ya so"

DALILI AKAN HAKA
Daga Abdillahi Dan Amru R.A yace:"Ya Manzon Allah Lallai Ladanai suna samun fifikon lada akan mu,Sai Annabi s.a.w ya ce:
*(Kuriqa fadar abinda yake fada lokacin kiran Sallah,idan angama kiran Sallah sai ku roki Allah za'a amsa maku)*.
@سنن أبي داود.

Annabi s.a.w yana cewa:
*(Adduar da akayi tsakanin kiran Sallah da Iqama ba'a mayar da ita"wato karbabbiya")*.
@الترمذي

Yan uwana muyi kokari wajan koyi da wannan Sunnoni da kiran yan uwa akan suyi aiki da ita dan mu kasance cikin masu koyi da bin Sunnar Annabi s.a.w na gaskiya.
@الوابل الصيب من الكلم الطيب ... ص 188


    Allah ne mafi sani


Load disqus comments

0 Comments

 

Random Posts

3/random/post-list
X

Contact Form

Name

Email *

Message *