HotBreaking News
Fetching data...

GANIN ALLAH ﷻ A RANAR ALQIYAMA

GANIN ALLAH ﷻ  A RANAR ALQIYAMA

الـعَلّامَـة ابْـنُ عُثَيْـمِينْ -رَحِـمَه الله-:
Yana cewa
Ranar alqiyama mutane sun kasu kashi uku game da ganin Allah ﷻ

KASHI NA FARKO
*(❶)_kashin farko su ne muminai zasu ga Allah ﷻ sau biyu a alqiyama, zasu gashi a lokacin yin hisabi da bayan sun shiga aljanna_*.
Allah ka sanya muna cikin su.

KASHI NA BIYU
*_(❷)Sune kafirai, su kuma ba zasu ga Allah ﷻ_* saboda dadin Allah ﷻ:-
{كلا إنهم عن ربهم يؤمئذ لمحجوبون﴾
Allah ka kare mu daga cikin su.

KASHI NA UKKU
*_(❸)Munafukai su kuma zasu ga Allah a lokacin hisabi sannan kuma a kange su daga ganin sa domin ba zasu shiga aljanna ba barantana suga Allah ﷻ wannan itace mafi girma hasara a gare su, domin an hana su ganin Allah na aljanna amma sun gashi a lokacin hisabi, saboda sun kasance suna baiyana musulunci a bakin su da zahiri amma suna boye kafirci,dan haka sai aka bar su suka ga Allah a lokacin hisabi kamar yadda suke bayyana Musulunci a fili kuma aka kangesu daga ganinsa a aljanna saboda ba zasu shiga aljanna ba kamar yanda suke boye kafirci_*.
@التعليق على صحيح المسلم (٦٠٥/١)



Allah ne mafi sani

Continue reading...

KYAKKYAWAN KARSHE

KYAKKYAWAN KARSHE

Kyakkyawan karshen dan adam shine mutum ya samu dacewa da aikata aiki mai kyau gab da karshen rayuwarsa sannan sai Allah ya karbi rayuwarsa bayan gama wannan aikin,ko yayi tuba ingantacce gab da rasuwarsa ko ya mutu yana aikata wani aiki mai kyau.

Daga Abi Umamah رضي الله عنه yana cewa,Manzon Allah ﷺya ce:-
*(Idan Allah yana nufin bawasa da alkhairi,sai Allah ya tsarkake shi kafin mutuwarsa)* Sai muka tambayi Manzon Allah ﷺ Minene tsarkake shi??? Sai yace:-
*(Sai ya datar da shi akan wani aiki mai kyau har zuwa ya karbi ransa akansa)*
@صححه_الألباني

        Allah ne mafi sani

*Allah ka sanya muyi kyakkyawan karshe ka sanya mu hadu da babban Masoyin mu Annabi Muhammad ﷺ a cikin aljanna,AMIN*.

Continue reading...

NA AMSHI KUDINSA, AMMA NA KI ZABARSHI ?

*NA AMSHI KUDINSA, AMMA NA KI ZABARSHI ?*
*Tambaya*
Assalamu alaikum, Malam Dan Allah ina da tambaya Dan siyasa ya bani kudi na zabe shi na karbi kudin, kuma ban zabe shi ba, mene ne matsayin kudin in naci?
*Amsa*
Wa'alaikumus salam To Gaskiya a fahimtata, in ka tabbatar ba za ka zabe shi ba, bai halatta ka amshi kudinsa ba, saboda Annabi S.A.W. yana cewa: "Musulmai Suna kan sharudansu" kamar yadda Bukhari ya ambace shi kuma Albani ya inganta shi a Irwa'ul galil hadisi mai lamba ta : 1743 ..
Sannnan kamar yadda ya haramta a ci dukiyar musulmai ba bisa hakki ba, haka ya haramta a ci dukiyar arne ba bisa hakki ba, ga shi kuma yaudara alama ce daga cikin alamomin munafuki, kamar yadda hadisai suka tabbatar.
Yana daga cikin ma'anonin dimukuraddiya zaben wanda Kake so, don haka babu bukatar boye-boye.
Allah ne mafi sani.
*Dr. Jamilu Zarewa*

Continue reading...

MAI WASA DA SALLAH IDAN BAKA TUBABA KANA CIKIN HADARI MAFI GIRMA

*_MAI WASA DA SALLAH IDAN BAKA TUBABA KANA CIKIN HADARI MAFI GIRMA_*.

Sallah dayace daga cikin rukunnan musulinci guda biyar wanda musuluncin bawa baya cika har ya tsayar da ita.
@Muslim

Mazon Allah SAW yana cewa:
*(Tsakanin mutum da tsakanin shirka da kafirci,shine barin Sallah).*
@Muslim

¤Manzon Allah SAW yana cewa:
*(Alqawalin da yake tsakanin mu da kafurai itace sallah, dukkan wanda ya bar sallah to ya kafirta).*
@ﺳﻨﻦ ﺍﻟﺘّﺮﻣﺬﻱ ﻭﻏﻴﺮﻩ

¤Imam Tirmizy ya ruwaito daga Abdillahi bn Shaqeeq al'uqaily yace:
*"Sahabban Annabi Muhammad saw basu ganin barin aiki wani aiki kafircine inbanda sallah".*
@ﺍﻟﺘّﺮﻣﺬﻱ .

Wato sun hadu akan dukkan wanda yabar sallah kafirine.
¤Manzon Allah SAW yana cewa:
*(Farkon abinda za'ayi wa bawa hijabi akansa na aiyukansa shine sallah,idan tacika tayi kyau ya tsira kuma ya rabauta,idan batayi kyauta kuma bata cika ba ya halaka ya tabe,idan an sami naqasa acikin farilla, sai Allah yace:kuyi dubi shin bawana ya sallolin nafila,sai ku cike gubin farillah da ita,sannan sauran aiyuka su kasance kamar haka)*.
@ﺍﻟﺘّﺮﻣﺬﻱ ﺃﻳﻀﺎ ﻭﻏﻴﺮﻩ.

¤Annabi SAW yana cewa:
*(Farkon abinda za'a fara yiwa bawa hijabi akansa na aiyukansa ranar alqiyama itace Sallah,idan tayi kyau to sauran aiyukansa ma sunyi kyau,idan ta baci sauran aiyukansa ma sun baci)*.
@ﻭﺭﻭﻯ ﺍﻟﻄّﺒﺮﺍﻧﻲ

¤Manzon Allah SAW yana cewa:
*(Wanda ya kiyaye Sallah yana da haske da hujja da tsira a gobe alqiyama, wanda kuma bai kiyaye sallah ba,baya da haske da hujja da tsira,aranar alqiyama yana tare da Qaruna da Hamana da fir'auna,da Ubaiyu bn Khalaf)*.
@ﻭﺭﻭﻯ ﺃﺣﻤﺪ ﻭﻏﻴﺮﻩ

_HUKUNCIN WANDA BAYA SALLAH_.

Wadanda basa yin sallah nau'i biyune:
1-Nafarko
*"Wanda ya bar yin sallah da gangam tare da kin yarda akan wajibcin sallah, wato bayayin sallah kuma yana ganin yin sallah ba wajibi bane,to wannan kafirine abisa haduwar dukkan musulmai baki daya, kuma kafircin da yake fitar da shi daga musulinci gaba daya".*

¤ﺍﺑﻦ ﺍﻟﻘﻴﻢ ﺭﺣﻤﻪ ﺍﻟﻠﻪ:
Yana cewa:
*"Babu sabani a tsakanin malamai cewar wanda ya bar yin sallar farillah da gangam,yana cikin mafi girman zunubi kuma laifine daga cikin manyan laifuka wanda yafi laifin kisan kai da fashi da makami,yafi laifin zina da da shan giya da dukkan wani laifi, kuma sakamakonsa shine halaka da tabewa da masifa tun daga nan duniya har zuwa lahira"*.

2-Na biyu
*"Wanda bayayin Sallah saboda kasala da ha'ince wani lokacin yayi wani lokacin yakiyi,amma tare da yardar cewa yin sallar wajibine,wannan shine yana cikin laifi mai girma kuma yana cikin alamar munafinci babba,mai wannan halin za'ayi masa nasiha da wa'azi cikin hikima.....".*

Malamai sun kasu kashi ukku akan mai wanann halin;-

i-Imam Malik da Shafi'i da Imam Ahmad awata riwaya daga wajansa,sun hadu akan cewa:
*"Mai wannan aikin ba kafiri bane amma yana cikin fasiqai za'a nemi ya tuba,idan ya tuba to idan kuma bai tubaba za'a kasheshi a matsayin Haddi da takobi".*

ii-Wasu daga cikin magabata sun tafi kaman yana zaman kafiri,wannan itace dayar riwayar Imam Ahmad da wasu daga cikin malaman Shafi'yya.

iii-Amma Imam Abu Hanifa ya tafi akan wanda baya sallah dan kasala da ha'inci tare da yarda da wajibancin Allah,cewa:
*"Baya zaman kafiri kuma baza'a kashe shiba sai dai za'a matsa masa har sai yayi Sallar".*

     Allah ne mafi sani.
*_Allah ka bamu ikon tabbatuwa akan yin sallah akan lokacinta kuma cikakkiya irinta Annabi SAW har zuwa mutuwarmu_*.


Continue reading...

KYAUTATAWA MIJI HANYACE TA SHIGA ALJANNA.

KYAUTATAWA MIJI HANYACE TA SHIGA ALJANNA.

Ki nemi yardar mijinki ta hanyar kyautata masa da kalamai masu dadi da aiyukan ibadar aure yin hakan zai shigar da ita aljanna insha Allah.

*Aiki dan kadan marar wahala zai janyo maki dauwama acikin aljanna*.

Manzon Allah ﷺ yana cewa;-
*(Shin bazan baku ba labarin Mata yan aljanna ba daga cikin ku?Mata masu yawan haihuwa wadanda suka iya soyayya,wadda idan tayi maka laifi zata dora hannunta akan naka,sannan sai tace ga hannuna nan akan hannunka bazan dauke hannuna ba akan naka ba har Sai ka daina fishi dani har sai ka yafe min)*.
@السلسله الصحيحه 3380.

Manzon Allah ﷺ yana cewa;-
*(Idan mace ta sallaci sallolin guda biyar na farilla,kuma tayi azuminci azuminta na farillah,kuma ta kiyaye farjinta daga zina,KUMA TAYI BIYAYYA DA KYAUTATAWA MIJINTA,za'ace da ita kishiga aljanna ta dukkan kofar da kikaga dama)*
@صحيح الترغيب 1932.

Manzon Allah ﷺ yana cewa;-
*(Baya I ga mace da tayi azumin nafila alhalin mijinta yanana har sai da izininsa)*
@صحيح ترغيب 613.

Manzon Allah ﷺ yana cewa;-
*(Idan mutum ya kirayi matarsa zuwa shimfidarsa sai taki :-*wa,ya kwana yana mai fishi ita,Mala'iku suna la'antarta har zuwa ta wayi gari)*
@صحيح مسلم 1434.

Allah ne mafi Sani.

*اللهم أصلح أحوالنا أجمعين*

Continue reading...

NA KASA BAMBANCE TSAKANIN JININ BARI DANA HAIHUWA, YAYA ZAN YI?

*_NA KASA BAMBANCE TSAKANIN JININ BARI DANA HAIHUWA, YAYA ZAN YI?_*


                           *Tambaya*
Assalamu alaikum. mallan nice nake yawan yin bari( misscariage)sai wata ya kama nayi al'ada anma ba kaman yanda na saba ganin jinin al'adarba domin kuwa bai zuwa da dan yawa kaman yanda nasaba ganin jinin al'ada bai wuce naganshi dis dis ba a wano toh mallam bayan kwana uku sai ya tsaya anma tundaga wan nan bansake ganin jinin ba kuma nayi gwajin ciki wanda akeyi na fitsari anma bai nunamin akwai ciki na bayan wani watan ya tsaya saina fara ganin jini shima ba yanda na saba ganin jinin al'ada ba sai ciwon ciki da mara qarni sosai gashi jajawur ga wani dan kitse da wani zare zare da yake fitowa: shin dan allah mallam ya zanyi na banbance jinin bari dana haila kasancewar nayi bari akai akai har sau 5 haihuwa 1.

                             *Amsa*
Wa'alaykumussalam, Duk jinin da kika gani a BARIN da kika yi bayan ciki ya kai wata hudu, sunansa jinin haihuwa, in kuma bai kai ba sunansa jinin bari wanda baya hana sallah.

Allah ne mafi sani

21/01/2017

Amsawa:-Dr. Jamilu Zarewa.

Continue reading...

Tambaya: Kudina Suna karuwa A jakata Alhali basu Kai Hakaba?

TAMBAYA
========
👇
Assalamu alaikum
Mlm y gida y aeki
: Daman tambayace zanyi ta wani abu da yake daure min kai ako dayaushe: Wato nakasance idan nasa kudi a jaka ta sai inga sun karu ko koma idan an bani canji sai inga ya qaru alhalin acan wurin da aka bani dai dai,ne ko kuma idan naje siyan abu bani da ishashshen kudin amma ina bude jaka ta sai inga kudin m harda saura: Abun tun baya damuna har y dawo yake damuna shine nake so inji y abun yake. Allah sakawa mlm d alkhairi




AMSA
=====
👇
 Tabbas hakan yana faruwa.
  Aljanu suna yiwa mutum irin wannan. Musamman ma mata.
 Mun taba samun case din wata mata da suke ajiye mata kudi, sai take dauka tana Amfanin gabanta dasu. Da tazo aure sai abin ya gagara, Aljanin yake cewa Wannan kudin da yake kawo mata ae sadakinta ne ya bata, kuma a yanzu haka ya Aureta Sannan babu mai rabata dashi, tinda ta amince ta zama matarsa, da taci Sadakinsa da baya amince ba, bazataci Sadakinsa ba.
 Sannan ya taba faruwa wani lokaci, wata Daliba ta, take gaya min cewar, taga kudi a cikin Akwatin kayan Sawarta, sai Nace ta kawo min kudin, da ta kawo, sai Mukaga kudin sababbi kakar, Muka sayi tabarmi da butochi muka Raba masallatai.
 Sabida haka, ki dena taba wannan kudin, ki sami wani malami mai Amana kina bashi kudin yana hidimar Addini dashi. Su masu kudin sai Allah yake kai musu ladan abinda aka Aiwatar, Sabida kudin ba nasu bane, dakkowa sukeyi a banki ko idan wani ya ajiye sai da dakko.

Allah shine masani.


ZAUREN FADAKARWA A SUNNAH MAZA MATA 08108605876
Continue reading...

ABUBUWAN DA YA KAMATA MACE MAI YARON CIKI TA KULA DA SU

*_ABUBUWAN DA YA KAMATA MACE MAI YARON CIKI TA KULA DA SU._*

*Tambaya*
Don Allah Malam wata tambaya aka yi min, shi ne na ke son a taimaka min wajan ba da amsa, tambayar ita ce : me ya kamata mai yaron ciki ta kula da shi?
*Amsa*
To malama akwai abubuwan da ya kamata mace ta kula da su, lokacin da take da ciki, ga wasu daga ciki:
1. Ki yi kokari, ki dinga cin halal, saboda lokacin da yaro yake ciki, na daga cikin lokutan da yaro yake ginuwa, don haka, idan kina cin haramun, yaron zai ginu da ita, sai Allah ya fara cirewa gabobinsa son alkhairi, tun yana yaro, domin duk jikin da ya ginu da haramun zai zama mai kasala wajan aikata abin da Allah yake so, kamar yadda malamai suka yi bayani.
2. Wasu malaman suna cewa : yawan saduwa yana karfafa yaro a ciki, saboda Annabi s.a.w ya kamanta ciki da shuka, kamar yadda ya zo a hadisin Abu dawud, mai lamba ta: 1847, kuma shuka tana kara karfi duk lokacin da aka bata ruwa.
3. Neman masa tsari daga shaidan, kamar yadda mahaifiyar nana Maryam ta nemarwa 'yarta tsari, lokacin da ta haife ta.
4. Nisantar duk wani abu da zai cutar da shi, saboda musulunci ya yi umarni da kula da rai, don haka zai yi kyau a matsayinki na sabon aure, ki nemi shawarar magabata da kuma likitoci, saboda ki gujewa abin da zai cutar da yaronki.
5. Zuwa asibiti, lokaci-lokaci don tabbatar da lafiyar yaron.
Allah ne mafi Sani.
16\6\2014
Amsawa:-Dr. Jamilu Zarewa.
Continue reading...

LADUBBA GUDA 11 NA TILAWAR ALQUR'ANI

*_LADUBBA GUDA 11 NA TILAWAR ALQUR'ANI_*


Babu wani abu da yafi chanchantar a bashi ladabi da kyautatawa lokacin yinsa kamar Maganar Ta'ala wato Alqur'ani mai girma.

_Alqur'ani mai girma yana buqatar Ladubban da kyautatawa ta musamman lokacin karantasa da Tilawarsa da lokacin kokarin sanin ma'anoninsa_.

An tambayi babbar Majalissar bada fatawa ta kasar Saudiyya mai suna:
*""ﺍﻟﻠّﺠﻨﺔ ﺍﻟﺪﺍﺋﻤﺔ ﻟﻺﻓﺘﺎﺀ ﺑﺮﺋﺎﺳﺔ ﺍﻟﺸَّــﻴﺦُ ﺍﻟﻌﻠّﺎﻣــﺔ / ﻋـﺒﺪُ ﺍﻟـﻌَﺰِﻳـﺰ ﺑﻦ ﺑـﺎﺯ - ﺭﺣﻤﻪُ ﺍﻟﻠﻪ ":-*

TAMBAYA
*_Wadan nene manyan Ladubban tilawar Alqurani mai girma??"_*.


AMSA:
Tilawar Alqurani mai girma tana da ladubba masu yawa,ga kadan daga cikinsu;-

*1-Mai Tilawar alqurani ya zama mai kyakkyawar Niyya da ikhlasy acikin karatunsa da neman yarda fuskar Allah da wannan tilawa tasa da nisantar dukkan wata Riya da Sum'a da neman dukiya ko neman ladar duniya da abin duniya da tilawarsa ta littafin Allah,ya zama yayi karatunsa ne da tilawarsa dan Allah shi kadai,dan neman kusanci zuwa gare sa shi kadai*.


2-Ya fara karatun alqur'ani da neman tsarin Allah daga shaidhan,sannan ya fadi:

ﺑـﺴﻢ ﺍﻟﻠﻪ ﺍﻟـﺮﺣﻤﻦ ﺍﻟـﺮﺣﻴﻢ .
Idan zai fara karatun sa ne daga farkon sura,in banda farkon Suratul Tauba,itace wadda ba'a karata-
ﺑـﺴﻢ ﺍﻟﻠﻪ ﺍﻟـﺮﺣﻤﻦ ﺍﻟـﺮﺣﻴﻢ
Lokacin da za'a fara karanta ta daga farko.

*3-An so mai karanta alqurani ya zama cikin alwala,idan zaiyi karatun ne daga littafin alquranin,to anan wajibine yayi alwala, awajan mafi yawan malamai magabata,saboda fadin Manzon Allah ﷺ* :
_(Babu mai taba alqurani sai mai tsarki)_.


4-An so ya zauna lokacin tilawar alqurani a kyakkyawan yanayi, yana mai sanya tufafai mafi kyau, yana mai fuskantar alqibla,kuma yayi tilawar a wajan da baza'a tozarta alqurani ba.


*5-Yana mai Tawali'u da nutsuwar zuciya da gabbai,lokacin tilawar alqurani,tare da yin tunani ga abinda kake karantawa na ayoyin Allah,tare da girmama maganar Allah*.

Kada ka yanke ayar alqurani dan yin magana da wani,sai dai ka ida ayar sannan kayi maganar idan ta kama dole.

6-Ya karanta alqurani dalla-dalla daki daki tare da baima kowani harafi hakkinsa lokacin karatu,domin kana karanta maganar Allah ce,ba maganar waninsa ba,tare da kiyaye Hukunce hukuncen Tajweedi gwargwadon iyawarka.


*7-Idan wani yana karatun alqurani a kusa da kai,ko wani yana sallah,to ka sassauta sautinka dan kada ka rikitasa wajan karatunsa*.


8-Kada yariqa karatun cikin sauri yadda zai kasance baima sannan me yake karantawa ba, ko yariqa yin jà mai yawa har ya riqa kara wani harafi wanda baya cikin littafin Allah,Kariqa yin karatu matsakaici.

*9-Kada ya riqa karanta alqurani da waken kida,kamar yadda Kirista sukeyi a chochi,ko da wani irin yanayi da sigar da tasabawa karatun magabata*.


10-Yana cikin manyan ladabin karatun alqurani,mutum ya tsaya da karatu idan hamma tazo alhalin yana tilawa,sannan sai yaci gaba idan ya gama hammar,dan girmama maganar Allah,domin hamma daga shaidhan take.


*11-Yana cikin Manyan ladabin tilawar Alqurani ka tsaya a wajan Ayar datake bayani akan Rahama,sai karoki Allah rahama,idan kazo wajan ayar da rake magana akan azaba da fishin Allah sai ka roki Allah ya kareka daga fadawa cikinsu,idan anzo wajan Tasbihi kayi tashihi koda acikin sallah ne,amma banda sallar Farillah*.


Idan kuma kazo wajan sujada kayi sujada koda kana cikin sallar farillane.
- ﺍﻟﻔﺘﻮﻯ ﺭﻗﻢ ‏( ١٨٦٧٦ ) ] .



      Allah ne mafi sani

Continue reading...

ABUBUWA GUDA 5 DA WATAQILA DAYAWANMU BAMUSAN WAYOYINMU NA TAFI DA GIDANKA SUNAYI BA

ABUBUWA GUDA 5 DA WATAQILA DAYAWANMU BAMUSAN WAYOYINMU NA TAFI DA GIDANKA SUNAYI BA

A yanayin neman taimakon gaggawa, wayar tafi-da-gidanka zata iya baka agaji ta kuma zamto silar ceton rayuwarka ko na waninka.

1. neman agajin gaggawa (Emergency Services) 🚑🚑🚑

Akwai number na Emergency duk duniya wanda kowacce wayar tafi-da-gidanka ka iya amfani dashi. Wannan number itace 112. Idan ka riski kanka a wajen da babu network, kuma ana buqatar taimakon gaggawa, kawai ka latsa 112 a lokacin. Wayarka zata searching dukkanin wani network dake wajen sannan ta baka emergency number da zaka kira. Wani abun burgewa ma shine koda wayar a kulle take da pattern ko pin, zaka iya latsa wannan emergency number din Wacce kyauta ake kira duk fadin duniya.

2. Shin makullin motarka ka manta ka kullesu acikin mota!

Idan ka kulle remote na motarka wanda baya dauke da key acikin motar kuma spare key yana gida, ka kira wani a gidan ta wayarsa da wayarka ta tafi-da-gidanka. Ka riqe wayar tafi-da-gidankan kamar dai-dai taqu daya daga jikin motar, saika umurci wanda ke gidan ya danna unlock button alhali yana riqe da remote din a daf karshen wayarshi ta daya bangaren da bai Kara kunneshi ba. Motarka zata budu. Idan kayi hakan ka ceci wani daga hawa Abin hawa ya kawo maka keys kuma kaima zaka saving lokacinka

3. Shin battery na wayarka ya zama empty ne?  Duk wayoyin battery power nasu sun 6oye? 📱📱📈📈

Domin dawo dasu, ka latsa  *3370#.. Ka aikata hakan yayinda wayar tana dafda daukewa domin rashin caji. Wayar taka zata restart ta wani hanya ta musamman na reserve inda zata nuna maka charging yakai 50%. Wannan reserve din zai kara charging kansa duk lokacin daka jona wayar taka a caji. Wannan sirrin yananan kusan a kowani manual na waya, sai dai dake muma manual ne muna tsallake karanta manuals na wayoyi muke amfani dasu.

4. Hana wayarka da'a ka sace amfani (Disabling)
📱❌📱❌📱❌📱

Domin duba serial number na wayarka, ka latsa: (*#06#).

Nambobi guda 15 zasu bayyana a screen handset dinka. Ka rubuta ka ajiye a diary ko wani waje. Idan akasamu akasi wani yadauki aron wayarka ba tareda saninka ba (sacewa),  ka kira service provider naka ka basu code din. Zasu blocking wayar, bazata amfani wanda ya dauka ba, kuma idan kayi sa'a akwai tracker dazai locating a ina wanda ya sace wayar taka yake. Codes dinma sunanan a rubuce a jikin Kowani kwalin waya. Don haka ana adana kwalin waya idan an saya saboda tsaro.

5. Dawo da ATM PIN Number (Reversal)
❌💰💵❌💰💵

Idan danfashi ko 6arawo yamaka matsin lamba akan sai Kunje ATM machine ka sanya pin dinka ka cire mar kudi, zaka iya sanar da police dake wajen ta hanya sanya pin naka na ATM a juye (misali 1234 ne pin din, sai ka sanya 4321 maimakon). Machine din zai iya baka kudin daka requesting, ammana nan take police zasu zo su shiga lamarin suyi ram da 6arawon. Kowani ATM machine yanada wannan emergency services din wanda dokace.

Ayi qoqarin yada irin wannan abu ga Yan'uwa da abokan arziki.
 BN ABBAS FOUNDATION

Continue reading...

KADA KAYI SUJADA HAR SAI LIMAN YAYI SUJADA

KADA KAYI SUJADA HAR SAI LIMAN YAYI SUJADA

Manzon Allah ﷺ yayi mana umarni akan koyi da liman akan a dukkan aiyukan sallah,kuma kada ka riga liman yin wani aiki na sallah,ko kuyi tare sai dai kayi bayan liman yayi.

Malamai sun kasan mabiya liman acikin aiyukan Sallah zuwa kaso ukku-

*_1-Akwai Yayayin Liman,wato wanda yake riga liman yin wani aiki na sallah,shi wannan baya da sallah,saboda ya saba umarnin da Manzon Allah ﷺ ya bada ga mai bin liman_*.

*_2-Sa'an liman,shine wanda suke aikata wani aikin sallah tare da liman,kamar sujada da ruku'u,mai wannan hali wani lokacin yana rasa ladar sallah koda sallar tasa bata baciba_*

*_3-Kanan liman,shine wanda yake aikata dukkan wani aikin sallah bayan liman yayi,wannan shine mai cikakken koyi da liman kuma mai bin umarnin Manzon Allah ﷺ,wannan shine mafi samun ladar sallah_*.

_KADA KAYAYI SUJADA DA DUKKAN AIYUKAN SALLAH SAI LIMAN YAYI_

Daga Barra'a bn Azib رَضِيَ اللَّهُ عَنْهُ yana cewa:
"Mun kasance muna yin sallah a bayan Annabi ﷺ idan yace:
[سمع الله لمن حمده]
babu daya daga cikin mu da yake sunkuyar da bayansa har sai Annabi ﷺ ya dora goshin a kasan da sujada".
@رواه البخاري رحمه الله في صحيحه.

Daga Muhaarib Bn disaar yana cewa;naji Abdullahi bn Yazid yana fada akan minbari:Barra'a رضي الله عنه yana cewa:
*_"Lallai su Sahabban Annabi ﷺ sun kasance suna Sallah tare da Annabi ﷺ,idan yayi Ruku'u sai muyi ruku'u,idan ya dago daga ruku'u sai yace_*:
_[سمع الله لمن حمده]_

*Bama gushewa muna tsaye har sai Manzon Allah ﷺ ya dora goshinsa a kasa yayi sujada,sannan muyi sujada a bayansa"*.
@مسلم

A wata riwayar yana cewa:
*"Mun kasance tare da Annabi ﷺ acikin sallah,dayan mu baya motsa bayansa dan tafiya sujada har sai munga Manzon Allah  ﷺ ya riga yayi Sujada"*.
 
A wata riwayar daga Abi Hurairata رضي الله عنه yace:Manzon Allah ﷺ yace:
*(Kada kuyi ruku'u har sai liman yayi ruku'u,kuma kada kuyi sujada har sai yayi sujada....)*.

  Allah ne mafi sani


_Allah ka bamu ikon koyi da bin umarnin Manzon Allah ﷺ a dukkan rayuwar mu baki daya_.

Continue reading...

MANHAJIN SHAIKH IBNU BAAZ YANA RADDI GA MANHAJIN KUNGIYAR SALAFIYYUN

MANHAJIN SHAIKH IBNU BAAZ YANA RADDI GA MANHAJIN KUNGIYAR SALAFIYYUN
Manhajin Shaikh Ibnu Baaz na Nasiha da inkarin Munkari ya banbanta da Manhajin Masu Guluwwi a Bidi'antarwa, saboda nasa Manhajin na Shari'a ne, amma nasu kuma kirkirarren Manhaji ne da aka labe a bayan Ilimin "Jarhi da Ta'adili" ana barna da raba kan Ahlus Sunna da zaluntarsu da shi.
Shaikh Ibnu Baaz ya ce:
ﺍﻟﺒﻴﺎﻥ ﺍﻟﺬﻱ ﺃﺷﺎﺭ ﺇﻟﻴﻪ ﺍﻟﺴﺎﺋﻞ ﺃﺭﺩﻧﺎ ﻓﻴﻪ ﻧﺼﻴﺤﺔ ﺇﺧﻮﺍﻧﻲ ﺍﻟﻌﻠﻤﺎﺀ ﻭﺍﻟﺪﻋﺎﺓ ﺑﺄﻥ ﻳﻜﻮﻥ ﻧﻘﺪﻫﻢ ﻹﺧﻮﺍﻧﻬﻢ ﻓﻴﻤﺎ ﻳﺼﺪﺭ ﻣﻦ ﻣﻘﺎﻻﺕ ﺃﻭ ﻧﺪﻭﺍﺕ ﺃﻭ ﻣﺤﺎﺿﺮﺍﺕ ﺃﻥ ﻳﻜﻮﻥ ﻧﻘﺪﺍ ﺑﻨﺎﺀ ﺑﻌﻴﺪﺍ ﻋﻦ ﺍﻟﺘﺠﺮﻳﺢ ﻭﺗﺴﻤﻴﺔ ﺍﻷﺷﺨﺎﺹ؛ ﻷﻥ ﻫﺬﺍ ﻗﺪ ﻳﺴﺒﺐ ﺷﺤﻨﺎﺀ ﻭﻋﺪﺍﻭﺓ ﺑﻴﻦ ﺍﻟﺠﻤﻴﻊ .
ﻭﻛﺎﻥ ﻣﻦ ﻋﺎﺩﺓ ﺍﻟﻨﺒﻲ ﺻﻠﻰ ﺍﻟﻠﻪ ﻋﻠﻴﻪ ﻭﺳﻠﻢ ﻭﻃﺮﻳﻘﺘﻪ ﺇﺫﺍ ﺑﻠﻐﻪ ﻋﻦ ﺑﻌﺾ ﺃﺻﺤﺎﺑﻪ ﺷﻲﺀ ﻻ ﻳﻮﺍﻓﻖ ﺍﻟﺸﺮﻉ ﻧﺒﻪ ﻋﻠﻰ ﺫﻟﻚ ﺑﻘﻮﻟﻪ ﺻﻠﻰ ﺍﻟﻠﻪ ﻋﻠﻴﻪ ﻭﺳﻠﻢ : ‏« ﻣﺎ ﺑﺎﻝ ﺃﻗﻮﺍﻡ ﻗﺎﻟﻮﺍ ﻛﺬﺍ ﻭﻛﺬﺍ ‏» ﺛﻢ ﻳﺒﻴﻦ ﺍﻷﻣﺮ ﺍﻟﺸﺮﻋﻲ ﻋﻠﻴﻪ ﺍﻟﺼﻼﺓ ﻭﺍﻟﺴﻼﻡ ...
ﻓﻤﻘﺼﻮﺩﻱ ﻫﻮ ﻣﺎ ﻗﺎﻟﻪ ﺍﻟﻨﺒﻲ ﺻﻠﻰ ﺍﻟﻠﻪ ﻋﻠﻴﻪ ﻭﺳﻠﻢ ﺃﻱ ﺃﻥ ﺍﻟﺘﻨﺒﻴﻪ ﻳﻜﻮﻥ ﺑﻤﺜﻞ ﻫﺬﺍ ﺍﻟﻜﻼﻡ، ﺑﻌﺾ ﺍﻟﻨﺎﺱ ﻗﺎﻝ ﻛﺬﺍ، ﻭﺑﻌﺾ ﺍﻟﻨﺎﺱ ﻳﻘﻮﻝ ﻛﺬﺍ، ﻭﺍﻟﻤﺸﺮﻭﻉ ﻛﺬﺍ، ﻭﺍﻟﻮﺍﺟﺐ ﻛﺬﺍ ﻓﻴﻜﻮﻥ ﺍﻻﻧﺘﻔﺎﺩ ﻣﻦ ﻏﻴﺮ ﺗﺠﺮﻳﺢ ﻷﺣﺪ ﻣﻌﻴﻦ، ﻭﻟﻜﻦ ﻣﻦ ﺑﺎﺏ ﺑﻴﺎﻥ ﺍﻷﻣﺮ ﺍﻟﺸﺮﻋﻲ، ﺣﺘﻰ ﺗﺒﻘﻰ ﺍﻟﻤﻮﺩﺓ ﻭﺍﻟﻤﺤﺒﺔ ﺑﻴﻦ ﺍﻹﺧﻮﺍﻥ ﻭﺑﻴﻦ ﺍﻟﺪﻋﺎﺓ ﻭﺑﻴﻦ ﺍﻟﻌﻠﻤﺎﺀ ....
ﻓﻨﺼﻴﺤﺘﻲ ﻟﻠﺠﻤﻴﻊ ﺃﻥ ﻳﻜﻮﻥ ﺍﻟﺘﺨﺎﻃﺐ ﻓﻴﻤﺎ ﻳﺘﻌﻠﻖ ﺑﺎﻟﻨﺼﺤﻴﺔ ﻭﺍﻟﻨﻘﺪ ﻣﻦ ﻃﺮﻳﻖ ﺍﻹﺑﻬﺎﻡ ﻻ ﻣﻦ ﻃﺮﻳﻖ ﺍﻟﺘﻌﻴﻴﻦ ﺇﺫ ﺍﻟﻤﻘﺼﻮﺩ ﺍﻟﺘﻨﺒﻴﻪ ﻋﻠﻰ ﺍﻟﺨﻄﺄ ﻭﺍﻟﻐﻠﻂ ﻭﻣﺎ ﻳﻨﺒﻐﻲ ﻣﻦ ﺑﻴﺎﻥ ﺍﻟﺼﻮﺍﺏ ﻭﺍﻟﺤﻖ ﻣﻦ ﺩﻭﻥ ﺣﺎﺟﺔ ﺇﻟﻰ ﺗﺠﺮﻳﺢ ﻓﻼﻥ ﻭﻓﻼﻥ .
ﻣﺠﻤﻮﻉ ﻓﺘﺎﻭﻯ ﺍﺑﻦ ﺑﺎﺯ ‏( /7 315 - 316 )
"Bayanin da mai tambaya ya yi ishara gare shi Nasiha muka yi nufi a cikinsa ga 'yan uwana Malamai da Masu da'awa, a kan "naqadinsu" (raddi) ga 'yan uwansu a kan abin da yake kasancewa daga gare su a makaloli da "nadawa" (taron kara wa juna sani) da lakcoci da suke yi, ya kasance raddi ne na neman gyara, wanda ya zama NESA DA JARHI (SUKA) da KAMA SUNAYEN MUTANE, saboda wannan yana jawo gaba da kiyayya a tsakanin duka bangarorin.
Ya kasance daga cikin al'adar Annabi (saw) da tafarkinsa idan labarin wani abu ya same shi daga wani Sahabinsa, abin da ya saba Shari'a to zai fadakar a kan haka ne da fadinsa: "Me ya samu wasu mutane suka ce: kaza da kaza?" Sai ya bayyana yadda abin yake a Shari'a (saw)...
Don haka manufata a bayanin da na yi shi ne abin da Annabi (saw) ya fada. Ma'ana; fadakarwa a kan kurakurai ya kasance da irin wannar magana, a ce: wasu mutane sun ce kaza..., wasu mutane suna cewa; kaza..., amma abin da ya dace da Shari'a shi ne kaza..., abin da yake wajibi shi ne kaza..., sai yin raddin ya kasance ba tare da jarhi (suka) ga wani mutum sananne ba, sai dai a yi raddin a bisa babin bayanin abun a shar'ance, har a samu soyayya a tsakanin 'yan uwa, da malamai da masu da'awa...
Nasihata ga kowa da kowa; magana a kan abin da ya shafi Nasiha da raddi ya kasance ta hanyar saye suna ba ta hanyar kama sunan mutum ba, saboda manufar ita ce fadakarwa a kan kuskure, da abin da ya kamata na bayanin dadai da gaskiya, ba tare da bukatuwa ga sukan wane da wane ba".
Wannan shi ne Manhajin Shaikh Ibnu Baaz, wanda ya dace da Sunnar Manzon Allah (saw), sabanin Manhajin Kungiyar Salafiyyun, Manhajin da suka kirkira da sunan aiki da "Jarhi da Ta'adili", alhali ilimi ne da asali ya takaita ne ga maruwaita Hadisi kawai.

Continue reading...
 

Random Posts

3/random/post-list
X

Contact Form

Name

Email *

Message *