HotBreaking News
Fetching data...

KI ZAMO MAI TSAFTA

KIZAMO MAI TSAFTA


ﺑِﺴْﻢِ ﺍﻟﻠّﻪِ ﺍﻟﺮَّﺣْﻤَﻦِ ﺍﻟﺮَّﺣِﻴﻢِ

ﺍﻟﺤﻤﺪ ﻟﻠﻪ ﺭﺏ ﺍﻟﻌﺎﻟﻤﻴﻦ ،

 ﻭﺻﻠﻰ ﺍﻟﻠﻪ ﻋﻠﻰ ﻣﺤﻤﺪ ﻭﻋﻠﻰ ﺁﻟﻪ ﻭﺻﺤﺒﻪ ﺃﺟﻤﻌﻴﻦ، ﻭﺑﺎﻟﻠﻪ ﺍﻟﺘﻮﻓﻴﻖ


السلام عليكم ورحمة الله وبركاته

KI ZAMO MAI TSAfta 

Mijinki yanason matarsa takasance mai tsafta kuma kyakkyawa,


 domoin shi (mijin)

idan ya fita yana ganin wasu al'amura na fitina da rudu awajen wasu mata.

kada shaidan ya rinjayeki er uwa matar aure game da mijinki ya hanaki kula dashi da tsaftar tsafta da kwalliya.


Ki zamo a gidanki ko da yaushe kamar amarya ta hanyar tsaftace gidanki da kawar da duk wani gashi da akeso ki kawar ta tsaftace jiki da ruwa domin Ruwa shine mafi kamshin turare,


 Abin rasawa kamar yadda wata Balarabiya tace da erta kafin ita kuma Allah ya sanar damu(Hakika Allah yana son masu tuba da masu tsarki)

qur'an(2:222.)


Daga nan Allah ya umarci mace tayi wanka bayanta gama jinin Al'ada kona haihuwa da gusar da warin  jini ta yadda mijinta bazai cutu da itaba,

barima inace miki er uwa:

Mala'iku ma suna cutuwa da abinda mijinki yake cutuwa dashi.


Saboda haka kiyi kwadayin abinda zaixo👇

@Kiyi wanka  na musamman musamman kafin ki kwanta.


@Ki kamsasa gurin baccinku.


@Kiyi amfani da abubuwan da mijinki yake so na daga kwalliya.


@Ki tsaftace tufadinki ki kuma kamsasa kayan.


@Lura da baki da kuma kamshinsa kiyi amfani da asuwaki ko man goge baki.


@Kawar da duk wani gashi na jiki kibar gurin da fitowar gashi agurin yake Ado.


@Ki ware turaren baccinki daban da sauran wanda zakisa ba lokacin bacciba ki zama mai sanyin kamshi ba mai hawa kaiba.


Sai dai ni er'uwa ba ina nufin ki nauyaya kafadar mijinki da abubuwa masu tsada bane ki daura masa abinda bazai' iyaba,

 awajen siyan kayan kwalliya da tufafi da kayan ado.


Barima kiyi kokarima ki zamo kyakkyawa kuma mai tsafta batare da kin dorawa mijinki avinda baxai'iyaba. 


KISSA DA KUMA ABIN LURA

Wani daga cikin malamai yana cewa:

Wani mutum yazo wajena yana so ya saki matarsa sai na tambatayeshi meye dalili da yasa xai saketa na ringa lallashinsa akan yayi hakuri kar ya saketa shi kuma yana kawo min dalilai masu yawa da yasa yake son sakinta dana takura mishima sai yace mini warin Jininta baya tafiya🙊

 ma'ana ko da yaushe yananan ko bayan ta gama al'ada.


Er uwa!Dazaki kamsasa jikinki da kuma kyawunki na zahiri (tsafta)suna tasiri a zuciyar mijinki kiyi kwadayi akan haka zaki mallaki zuciyar mijinki Insha Allah 😊.


سبحانك اللهم وبحمدك أشهد أن لا إله إلا انت أستغفرك وأتوب إليك.


Zamu ci gaba insha Allahu


Rubutawa✍🏼

{-Aysha mika'il-Idris Bichi-}

Ummu Ammarah,

Continue reading...

TA YAYA ZAN IYA GANE MUKTARIN SALLAH DA LALURINTA?

*_TA YAYA ZAN IYA GANE MUKTARIN SALLAH DA LALURINTA?_*

*Tambaya*

Assalamcualaika mal da Allah amin bayanin yadda ake gàne yanayin muhktari da lalurin sallan Asuba da maghrib

*Amsa:*

Wa'alaikum assalam, Muktari da laluri, lokuta ne da Allah ya rataya hukunce-hukuncen sallah akan şu, a na gane muktarin sallar asuba idan alfijir na biyu ya keto, ana gane lalurin sallar asuba idan gari ya yi fayau, an gane muktarin sallar azahar idan rana ta karkata daga tsakiyar sama, ana gane lalurin sallar azahar idan inuwar mutum ta yi daidai da tsawonsa, ana gane lokacin la'asar zababbe ya shiga idan inuwar mutum ta yi daidai da tsawonsa, ana gane lalurinta ya shiga idan inuwar mutum ta ninka tsawonsa, ana gane muktarin sallar magriba, idan rana ta fadi, Muktarin sallar Isha yana shiga idan ragowar Jan rana ya buya (shafaki) Bayan dare ya raba lokaci ne na lalurin magriba da Isha.

Allah ne mafi Sani.

Amsawa:-Dr. Jamilu Zarewa.

Continue reading...

AMSOSHIN TAMBAYOYIN DA BARRISTER BULAMA BUKARTI YA AIKEWA KUNGIYAR IZALA TA JIHAR KANO (4)

AMSOSHIN TAMBAYOYIN DA BARRISTER BULAMA BUKARTI YA AIKEWA KUNGIYAR IZALA TA JIHAR KANO  (4)


Tanbihi: Ba lallai ka fahimci cikakken sakonmu ba matukar baka karanta rubutu na 1, 2 da 3 ba.


Kafin naje zuwa ga amsa ta gaba, zanso na fadada bayani akan gaba ta kusa da ta karshe acikin rubutun da ya gabata.


A wajenmu, da wajen Barista, har yanzu sunan abinda ake yiwa Ganduje 'TUHUMA', tunda ba'a je karshen bincike ba. Ita kuma tuhuma da ta shafi mai imani, akwai abubuwan da akayi mana umarni dayi a yayinta. Ga su kamar haka:


1. Anyi mana umarnin kai tsaye ma mu karyata duk wata hutuma da aka yiwa masu imani, domin yi musu kyakkyawan zato. Saboda fadin Allah madaukaki:

 

لَوْلا إِذْ سَمِعْتُمُوهُ ظَنَّ الْمُؤْمِنُونَ وَالْمُؤْمِنَاتُ بِأَنفُسِهِمْ خَيْرًا وَقَالُوا هَذَا إِفْكٌ مُّبِينٌ


Ma'ana: Mene yasa lokacin da muminai maza da muminai mata sukaji (tuhumar da ake yiwa daya daga cikinsu) basu yiwa junansu kyakkyawan zato ba? Kamata yayi suce 'tsarki ya tabbata ga Allah, wannan kagaggiyar karya ce mabayyanina'.


2. An umarcemu da kame baki daga yada abinda yake na tuhuma ga masu imani, saboda Fadin Allah madaukaki:


وَلَوْلا إِذْ سَمِعْتُمُوهُ قُلْتُم مَّا يَكُونُ لَنَا أَن نَّتَكَلَّمَ 

 بِهَذَا سُبْحَانَكَ هَذَا بُهْتَانٌ عَظِيمٌ


Ma'ana: mene yasa lokacin da kukaji tuhumar, ba kuce 'bai kamata  muyi magana mu tattauna akan wannan batun ba, tsarki ya tabbata ga Allah, wannan karya ce mai girma.


3. Allah ya umarcemu kada mu kara jifan junanmu da wani abu na tuhuma, a inda yace:


يَعِظُكُمُ اللَّهُ أَن تَعُودُوا لِمِثْلِهِ أَبَدًا إِن كُنتُم   مُّؤْمِنِينَ


Ma'ana: Allah yana muku wa'azi/gargadi akan kada ku kara komawa zuwa ga jifan juna da abu na tuhuma, IN DAI KU MASU IMANI NE.


In dai sunan abinda ake yiwa gwanma 'tuhuma', toh ga maganar Allah akan tuhumar, ya rage na mutane suyi biyayya ko su saba.


Wani zai iya cewa ai wadannan ayoyin sun sauka ne akan Nana A'isha, saboda haka ba za'a iya kafa hujja dasu a irin wannan mas'alar ba.


Sai muce ko kadan ba haka abin yake ba. Tabbas wadannan ayoyin sun sauka ne akan Nana A'isha, amma  kuma zasu cigaba da yin aiki a duk sanda aka samu irin waqi'ar ko makamanciyarta. In kuwa ba haka ba, toh kenan babu wata aya ko daya da zamuyi aiki da ita a yanzu, tunda a asali ba akanmu ayoyin suka sauka ba, ko burbushinmu babu a lokacin. 


Na fadi hakan ne bisa dogaro ga wata QA'IDAH USULIYYA da take cewa: العبرة بعموم اللفظ لا بخصوص 

السبب

 Wato idan nassi yazo, me akace a nassin ake dubawa, ba asalin abinda ya faru nassin ya sauka ba


TAMBAYA TA UKU: Mallam yace "Ganduje ya hada kan malamai masu banbancin ra'ayi da fahimta, ta hanyar hadasu a wajen aiki daya, a saka dan izala shugaba, mataimaki dan darika..." toh dama rikicin malamai ba akan tauhudi da aqida bane? Dama akan rashin basu mukamai ne?


AMSA: ya salam!  Ko kadan bah aka abin yake ba, kuma shi kanshi Barista yasan ba hakan bane, amma ga amsar tambayar ka kamar haka:


1. Da farko dai hadin kai tsakanin mabanbanta akidu don zaman lafiya ba bakon abu bane a duniyar musulunci , kuma babban abin koyi akan haka shine shugaban mu Annabi MUHAMMAD (SAW), kamar yadda takardar yarjejeniyar zaman lafiya tsakanin musulmai da yahudawa da aka rubuta ta kunsa,  kuma manzo saw ya amince da ita.


2. Kungiyar izala karkashin jagorancin Dr. PAKISTAN itace ta fara mika hannu ga jagororin tijjaniyya da na qadiriyya da nufin rage zafin gaba da qiyayya tsakanin mabiya,  ba tare da kowa ya bar aqidar saba,  saboda koyi da abinda manzon Allah ya yi a madinah, kuma ba shakkah wannan ya bada gagarumar gudunmawa wajan raguwar fitintinu tsakanin kungiya da mabiya wadancan dariku, alhamdulillahi.


3. Idan muka dubi wadannan bayanai da suka gabata,  zamu yarda cewa  duk wani yunkuri na karfafa zaman lafiya da dakile fitintinu ya  cancanci a goya masa baya,  a yabawa maiyi kuma ayi masa fatan alkhairi, wannan shine abinda kungiya ta yiwa gwamna Ganduje, saboda kowa yana bada gudunmawar sane da irin damar da yake da ita, don haka yayi amfani  da kasancewarsa gwamna ya jawo wadannan malaman ya hada su guri guda don cimma wanacan buri. 


Dan haka maganar cewa dama rashin nadasu mukamai ne yake  jawo taqaddama a baya, inaga kodai rashin sanin abinda manzon Allah yayi a Madina, ko kuma rufe ido daga abinda malam Pakistan yai ta faman yi tun lokacin da gwamna bai zama gwamna ba, in kuwa ba haka ba, wanne mukami malam Pakistan yake nema a wancan lokacin kuma a wajan wa?


Dole ne dukkanmu mu fahimci cewa yin nesa da juna yana daga abinda yake kara iza wutar fitina tsakanin al’umma. Amma matsowa kusa yakan bayar da gudunmawa wajen kulla alaka, zumunci, jin kunyar juna, da kuma tattaunawa cikin laluma ta hanyar ilimi da hujjoji. Kenan zama ko aiki waje daya yana bada gudunmawa wajen hadin kai.


Ina fata barista da duk wanda ke bukatar fahimtar wannan ma'salar ya fahimta.


Allah yasa mu dace.

Zamu karasa tambayoyin nan ba da jimawa ba insha Allah.


Awaisu Al'arabee Fagge

Chairman Jibwis

Social Media

Kano State.

29-11-2018

Continue reading...

AMSOSHIN TAMBAYOYIN DA BARRISTER BULAMA BUKARTI YA AIKEWA DA KUNGIYAR IZALA TA JIHAR KANO (3)

AMSOSHIN TAMBAYOYIN DA BARRISTER BULAMA BUKARTI YA AIKEWA DA KUNGIYAR IZALA TA JIHAR KANO (3)


(Wanda bai karanta rubutu na 1 da na 2 ba, yanada kyau ya koma ya karanta, rashin karantawar zai hana shi ÿancin yance hukunci).


TAMBAYA TA BIYU: Annabi SAW ya kauracewa Nana A'isha a lokacin da ake tuhumarta, to a ina su Mallam suka samo sunnar kusantar Ganduje a lokacin da ake tuhumarsa?


AMSA: Gaskiya ne, Annabi SAW ya kauracewa Ummuna A'isha R.A a lokacin da munafukai suka jefeta da aikata alfasha, amma wannan ba zai zama dalili akan cewa dukkan mai lefi ne shari'ah ta wajabta a kaurace masa ba, na fadi hakan ne saboda dalilai kamar haka:


1. Ita Nana A'isha mata ce ga Annabi SAW, sai ake tuhumarta da aikata alfasha 'Wal Iyazu Billah', to a matsayinsa na mijinta wanda bai san gaibu ba, dole ne zai kaurace mata, saboda kusantarta zai zamanto matsala, koda wata mu'amala ta auratayya ta gudana tsakaninsu, kuma Allah ya kadarci samun wani rabo, to wannan rabon zai zamanto abin yiwa zargi da yar da magana, musamman a wajen munafukai...


2. Abinda zaisa mu fahimci cewa kauracewar da yayi mata yayi ne a matsayinsa na mijinta shine: bai yiwa kowane musulmi umarnin ya kaurace mata ba. Shiyasa a hadisin bamu samu mahaifiyarta da mahaifinta da sauran mutane sun kaurace mata ba.


3. Inda ace kaurace mata hukunci ne gamamme, da mahaifinta, wanda yake shine mutum mafi girma a duniyar musulunci bayan Annabi SAW, da ya kaurace mata, saboda yafi kaunar Annabi SAW fiye da ita.


4. An saukar da hukuncin kauracewa akan sahabbai guda uku da suka ki zuwa yaqi, KA'AB BN MALIK, HILALU BN UMAYYATA da MURARATU BN RABI'E, amma dayake su nasu hukuncin gamamme ne, daga kan Annabi SAW har zuwa kasa, babu wani mahalukin da yake kusantarsu, koda kuwa ta hanyar cinikayya ne. Don har daga karshe ma akayi umarnin matansu su fice sukoma gidajensu. Saboda nasu hukuncin gamamme ne.


5. Ta yadda zamu kara gane cewa ba akan kowanne abu yake zama wajibi a kauracewa mutum ba, ai idan muka tuna, zamu ga cewa an samu wasu cikin wadanda suka rayu da Annabi SAW, wasu sunyi zina, wasu sun sha giya, wasu sunyi sata, da makamantansu, toh Barista ai kaga wannan ba tuhuma bace, tabbas ne ma, amma ba'a yiwa al'umma umarnin su kaurace musu ba.


In short, ba akan kowanne laifi ake kauracewa mutum ba.


A NAN INASO NACE WANI ABU...


A fahimtarmu har yanzu muna a level ne na TUHUMA, koda a yaren su Barista, sai de ace 'ana tuhumar Gwamna...' ita kuma tuhuma a musulunci ma umarni akayi mana da yiwa masu imani kyakkyawan zato akanta, mu guji saurin yarda da ita. Duk wanda ya nazarci ma'anonin ayoyin da suka sauka domin Wanke Nana A'isha, zai fahimci hakan. (a duba farkon Suratun-nur).


Sannan wani abu da ya bani mamaki, Dr. Pakistan acikin jawabinsa yake cewa ai dama an tuhumci Nana Aisha da kuma Annabi Musa, sai Barista yake ganin kamar Dr. Ya kamanta Nana Aisha da Annabi Musa da Ganduje, amma kuma sai ga Barista yana hada alaka ta hanyar basa misali da kauracewar Annabi SAw ga Nana A'isha da kuma rashin kauracewar Izala ga Ganduje. Toh muma muna da tambaya: 


Menene hikimar hada wannan misalin?


Shin Barista yana kamanta Manzon tsira ne da Pakistan?


Zamu cigaba nan ba da dadewa ba insha Allah.


Awaisu Al'arabee Fagge

Chairman, Jibwis

Social Media

Kano State.

28-11-2018

Continue reading...

AMSOSHIN TAMBAYOYIN DA BARRISTER BULAMA BUKARTI YA AIKEWA DA KUNGIYAR IZALA TA JIHAR KANO (2)

AMSOSHIN TAMBAYOYIN DA BARRISTER  BULAMA BUKARTI YA AIKEWA DA KUNGIYAR IZALA TA JIHAR KANO (2)


Tanbihi:

1- Duk wanda bai karanta rubutun farko ba, to zaiyi kyau ya koma ya bibiya. Rashin bibiyar zai hanaka fahimtar sakon yadda yakamata.


2- Ban shardantawa kaina amsa tambayoyin Barista kamar yadda yayisu ba, saide zan fara dauko mafi muhimmanci daga cikinsu ne, koda ba dasu ya fara ba.


TAMBAYA TA DAYA: Menene hikimar kawo misalin Kazafin da aka yiwa Nana A'isha RA da Annabi Musa AS? Ko malam yana kamanta Nana A'isha  da Annabi Musa ne da Ganduje? Sannan hakan bai yi kama da abinda Malam Jafar yayiwa raddi ba a lokacin da aka kamanta jifan da aka yiwa Annabi SAW a Da'ef; da kuma wanda aka yiwa Atiku a Kano???


Amsa: Da farko dai muna cewa: أعوذ بالله من الشيطان الرجيم,  Allah ya tsari Dr. Pakistan da kamanta Annabi Musa da Nana A'isha da ganduje, nisan dake tsakaninsu yafi nisan sama da kasa. Haba mal. Bukarti! Ai koda an saba da Dr. akan ra'ayin siyasa ai ya kamata ayi masa kyakkyawan zato...


Sanannen abu ne cewar mutane sukan bawa junansu hakuri ta hanyoyi daban-daban, daga ciki, akan tunawa mutum wani abin damuwa ko matsala da ya samu wadanda suka fishi girma da matsayi.


Misali, Idan wani malamin yaje yayi wa'azi mutane suka ki karba, sai a bashi hakuri ace masa ka tuna cewa Annabi Nuhu ma yayi shekara 950 yana wa'azi amma mutane ÿan kalilan ne suka karba. Yayin da kake wannan misalin; babu wani mutum mai adalci da zai jefeka da cewar ka kamanta wannan malamin da Annabi Nuhu AS. (هذه بتلك ).


Wannan shi yasa ake yiwa wadanda suka gamu da bala'in rashin lafiya wa'azi da abinda ya sami Annabi Ayyuba,  ake yiwa wanda ya hadu da bala'in batan d'ansa wa'azi da abinda ya sami Annabi yaqub, ko ayi wa'azi ga wanda ya hadu da bala'in hassadar yan uwa da abinda ya sami Annabi yusuf... 


Bawai dan a kamantasu da wadannan manyan bayin Allah ba a'a saide don a rage musu radadin musifar da ta same su ta hanyar nuna musu hakan ya taba samun wadanda sukafi su daraja da alkhairi.


Shi yasa ko a lokacin da malam yake magana ya ce ai an tuhumci wadanda sukafi gomna daraja a wajan Allah da kuma wajan  duk wani musulmin kirki, dan haka kirkinka, ko tsoron Allahn ka bai iya hana a jefa maka tuhuma ko ta gaskiya ko ba ta gaskiya ba, dan haka babu laifi a musulunci idan wani abin damuwa ya sami mutun a bashi hakuri ta hanyar tuna masa abinda ya taba samun wanda ya fishi daraja mai kama da abinda ya sameshi.


Dangane da amsar Marigayi Sheikh Ja'afar Allah yayi masa rahama, ga wadanda suka fadi abinda suka fada gameda abinda aka yiwa Atiku, in Barista zai tuna abinda aka dinga fada wanda kuma Sheikh Ja'afar ya bada amsa a kai, abinda akace shine 'an jefi Atiku kamar yanda aka jefi Annabi, shine malam ya yi tir da waccan kamancceceiya da ya fahimta ana kokarin yi, tsakanin Annabi SAW da Atiku , wal-iyazu billah. Ala kulli halin, misalan da muka bayar sun isa su fayyace niyyar Dr. Pakistan a jawabin da yayi.


Zamu tashi a tambaya ta biyu nan ba da jimawa ba insha Allah.


Awaisu Al'arabee Fagge

Chairman Jibwis Social

Media, Kano State.

27-11-2018

Continue reading...

AMSOSHIN TAMBAYOYIN DA BARRISTER BULAMA BUKARTI YA AIKEWA DA KUNGIYAR IZALA TA JIHAR KANO (1)

AMSOSHIN TAMBAYOYIN DA BARRISTER BULAMA BUKARTI YA AIKEWA DA KUNGIYAR IZALA TA JIHAR KANO (1)


Daga: Awaisu Al'arabee Fagge.

Shugaban Jibwis Social Media

Na jihar Kano.


Bismillahirrahmanirrahim.


Bayan haka, mun saurari wadansu tambayoyi guda 16 da Bar. Bulama Bukarti ya aikewa kungiyar Izala ta jihar Kano, da shugabanta, Dr. Abdullahi Saleh Pakistan, akan ziyarar da Kungiyar ta kaiwa Mai girma Gwamnan jihar Kano, Dr. Abdullahi Umar Ganduje. Hakan yasa muka dauki haramar mayar da amsoshi ga Bulama, domin ya waraka, kuma al'umar da suke da bukatar amsoshin da yayi suma su waraka.


 Amma kafin mu shiga bayar da amsa; muna da wadansu bayanai masu muhimmanci kamar haka:


1. Muna yabawa da godewa Bulama Bukarti, musamman yadda yayi amfani da usulubi da mai cike da girmamawa da mutuntawa ga shugabanmu, duk dayake baristan baya goyon bayan abinda shugaban namu yayi. Wannan abin a yaba ne. Mun gode.


2. Kasancewar Barista Bulama yace yayi tambayoyinsa ne ga Dr. Pakistan da kuma Kungiyar Izala Ta jihar Kano,  sai muka ga rashin dacewar shigowar Dr. Pakistan domin bayarda amsar, domin dalilai kamar haka:


  A) Barista bulama ya shigo ne bayan musayar sakonni tsakanin Dr. Pakistan da Dr. Gumi, kenan ba da shi akeyi ba, to bai dace ace Dr. Pakistan ne zai bashi amsa ba.


  B) Barista Bulama ya tura sakonsa ne a Social Media, Mu kuma mune muke magana da yawun kungiyar Izala a social media, kenan hurumin mu ne mayar da martani akan wannan batu, musamman dayake ni shugaban Social media din, da ni akaje waccan ziyara.


C) Dayake Bulama Bukarti lauya ne, nasan yana da masaniya akan cewa 'wani yakan iya kare hakkin wani, ya kan iya amsa tambayoyi a madadin wani, koda kuwa a fanni shari'a ne kotu'. Toh bukatar amsoshi ake, ko da daga bakin wanene, ba lallai sai Dr. Pakistan ba.


D) Ko da kasancewarmu ÿan social media bai bamu hurumin amsa wadannan tambayoyi ba, duk da haka akwai lemar da zamu iya fakewa, domin kuwa ni da nake rubutu, ina cikin EXCO na kungiyar izala a matakin jihar Kano, kuma tambayoyin da Barista yayi, yayisu ne ga Dr. Pakistan da kuma kungiyar Izala baki daya.


Da dan wannan tanbihi nake neman taimakon Allah wajen fara amsa tambayoyin Barista.


TAMBAYA TA FARKO DA KUMA AMSAR TA........


(Zamu tsaya anan, amma zamu cigaba anan gaba kadan, domin gudun yin rubutu mai yawan da zai wahalar da mai karantawa)


Awaisu Al'arabee Fagge.

Jibwis Social Media

Kano State.

26-11-2018

Continue reading...

HARAMCIN YIN PRE-WEDDING A MUSULUNCI

*HARAMCIN YIN PRE-WEDDING A MUSULUNCI*

Pre-Wedding Pictures/Videos suna Daga Cikin Abinda Yanzu Mafi Yawan Al'Ummar Hausa/Fulani, Ina Nufin Musulmai, Suka Mayar Kamar Addini.

Wannan Ko Shakka Babu Masiface Ga Duk Masoyinta Dama Masu Goyawa Abin Baya. Haka Kuma Sharrice Ga Al'Umma.

Pre wedding shi ne namiji da mace za su rinqa riqe Juna da rungumar juna ko sumbatar juna ana daukan su a hoto ko video, wannan yana Kasancewa ne duk kafin aure.

Wannan aiki Na pre wedding haramun ne, ba ya halatta ga muslimi ya yi shi, ko ya bada gudummawa wajen yin sa, ko da duk duniya ana yin sa. Saboda abubuwan da kefaruwa a lokacin yin sa.

*1- TABA MATAR DA BATA HALATTA A GARE KA BA:* Ya haramta ga namiji ko mace su taba juna, ba tare da aure ba, amma awajen Pre wedding picture wani zai dauki hoton nema yana sumbatar ta ko rumgumar ta, ko ya rike kugunta, Bayan kuma ba aure. Wannan bai halatta ba kuma koda ma ba sumbatarta yayi ba, haramunne yatabata.

ﻋﻦ ﻣﻌﻘﻞ ﺑﻦ ﻳﺴﺎﺭ ﺭﺿﻲ ﺍﻟﻠﻪ ﻋﻨﻪ ﺃﻥ ﺭﺳﻮﻝ ﺍﻟﻠﻪ ﺻﻠﻰ ﺍﻟﻠﻪ ﻋﻠﻴﻪ ﻭﺳﻠﻢ ﻗﺎﻝ " : ﻷﻥ ﻳﻄﻌﻦ ﻓﻲ ﺭﺃﺱ ﺃﺣﺪﻛﻢ ﺑﻤﺨﻴﻂ ﻣﻦ ﺣﺪﻳﺪ ﺧﻴﺮ ﻟﻪ ﻣﻦ ﺃﻥ ﻳﻤﺲ ﺍﻣﺮﺃﺓ ﻻ ﺗﺤﻞ ﻟﻪ " ‏( ﺭﻭﺍﻩ ﺍﻟﻄﺒﺮﺍﻧﻲ ﻭﺍﻟﺒﻴﻬﻘﻲ ‏) ، ﻭﻗﺎﻝ ﺍﻟﻤﻨﺬﺭﻱ " : ﺭﺟﺎﻝ ﺍﻟﻄﺒﺮﺍﻧﻲ ﺛﻘﺎﺕ ﺭﺟﺎﻝ ﺍﻟﺼﺤﻴﺢ " ‏( ﺍﻟﺘﺮﻏﻴﺐ ﻭﺍﻟﺘﺮﻫﻴﺐ 3/39 . ﻭﺻﺤﺤﻪ ﺍﻟﺸﻴﺦ ﺍﻷﻟﺒﺎﻧﻲ ﻓﻲ ﺳﻠﺴﻠﺔ ﺍﻷﺣﺎﺩﻳﺚ ﺍﻟﺼﺤﻴﺤﺔ ﺍﻟﻤﺠﻠﺪ ﺍﻷﻭﻝ ﺣﺪﻳﺚ ﺭﻗﻢ 326 ).

"Da'a soka wa mutum allura ta bakin karfe akan sa, shi yafi masa alkhairi da ya taba matar da bata halatta a gare shi ba."

*2- BAYYANAR DA TSIRECI:* wajen daukan wannan Pre wedding din, hoto ne ko video dole sai matar ta bayyanar tsirecin ta da kwalliyar ta, ta nunawa duniya cewa ita fa, ta hadu, Mai kyau ce, Bayan musulunci Ya hana mace ta bayyanar da kwalliyar ta face GA wadansu mutane. Kamar yadda Allah yace:

" ﻭَﻗُﻞ ﻟِّﻠْﻤُﺆْﻣِﻨَﺎﺕِ ﻳَﻐْﻀُﻀْﻦَ ﻣِﻦْ ﺃَﺑْﺼَﺎﺭِﻫِﻦَّ ﻭَﻳَﺤْﻔَﻈْﻦَ ﻓُﺮُﻭﺟَﻬُﻦَّ ﻭَﻟَﺎ ﻳُﺒْﺪِﻳﻦَ ﺯِﻳﻨَﺘَﻬُﻦَّ ﺇِﻟَّﺎ ﻣَﺎ ﻇَﻬَﺮَ ﻣِﻨْﻬَﺎ ....."

‏( ﺳﻮﺭﺓ ﺍﻟﻨﻮﺭ 31 )

"Kuma Kace ga muminai mata su rintse idanun su(daga Kallan mazan da na su halatta ba). Su kare farjin su kuma ka da su bayyanar da kwalliyar su, sai dai abin da ya bayyana ............"

*3- RASHIN KISHIN JUNA:* yin wannan aiki Yana nunawa cewa Ango baya kishin matar da zai aura Don haka zata iya cire hijabin ta, kirjin ta a bude, da hannaye ta da kafafuwan ta duk ta budewa duniya ta ganta, shi a wajen sa babu komai, ka ga baya kishin ta, ita ma bata kishin akan ta. Ya zama daiyus Manzon Allah yace daiyus ba zai shiga aljanna ba.

ﻋﻨﻦ ﺍﺑﻦ ﻋﻤﺮ ﺭﺿﻲ ﺍﻟﻠﻪ ﻋﻨﻪ ﺃﻥ ﺭﺳﻮﻝ ﺍﻟﻠﻪ ﺻﻠﻲ ﺍﻟﻠﻪ ﻋﻠﻴﻪ ﻭﺳﻠﻢ ﻗﺎﻝ " ﺛﻼﺛﺔ ﻻ ﻳﻨﻈﺮ ﺍﻟﻠﻪ ﻋﺰ ﻭﺟﻞ ﺇﻟﻴﻬﻢ ﻳﻮﻡ ﺍﻟﻘﻴﺎﻣﺔ : ﺍﻟﻌﺎﻕ ﻟﻮﺍﻟﺪﻳﻪ ، ﻭﺍﻟﻤﺮﺃﺓ ﺍﻟﻤﺘﺮﺟﻠﺔ، ﻭﺍﻟﺪﻳﻮﺙ .." ﺭﻭﺍﻩ ﺃﺣﻤﺪ ﺍﻟﻨﺴﺎﺋﻲ ﻭﻗﺎﻝ ﺍﻟﺸﻴﺦ ﺍﻷﻟﺒﺎﻧﻲ ﺣﺴﻦ ﺻﺤﻴﺢ ﺍﻧﻈﺮ ﺻﺤﻴﺢ ﺳﻨﻦ ﺍﻟﻨﺴﺎﺋﻲ ٢ / ١٤٥

Manzon Allah(S.A.W) ya ce: "Mutun uku Allah ba ya duban rahma gare su Ranar alkiyama: wanda ya ke wulakanta iyayan sa, na biyu mace mai kwaikwayan maza, na uku Addaiyus (mara kishin iyalin sa).

*4- YADA ALFASHA:* wannan Pre wedding din Yana daya daga cikin yada fasikanci a ban kasa, ta yadda mutum zai rungumi (ko kiss din) MATAR da bata halatta ba a gare shi, ya na nunawa duniya cewa yayi hakan ne don ku kalli fasikancin da ya yi.

ﻭَﻋَﻦْ ﺃَﺑِﻲ ﺍَﻟﺪَّﺭْﺩَﺍﺀِ ﺭَﺿِﻲَ ﺍﻟﻠَّﻪُ ﻋَﻨْﻪُ ﻗَﺎﻝَ : ﻗَﺎﻝَ ﺭَﺳُﻮﻝُ ﺍَﻟﻠَّﻪِ ﺻَﻠَّﻰ ﺍﻟﻠﻪُ ﻋَﻠَﻴْﻪِ ﻭَﺳَﻠَّﻢَ { ﺇِﻥَّ ﺍَﻟﻠَّﻪَ ﻳُﺒْﻐِﺾُ ﺍَﻟْﻔَﺎﺣِﺶَ ﺍَﻟْﺒَﺬِﻱﺀَ } ﺃَﺧْﺮَﺟَﻪُ ﺍَﻟﺘِّﺮْﻣِﺬِﻱُّ , ﻭَﺻَﺤَّﺤَﻪُ . .

Manzon Allah(S.A.W) yace: "Hakika Allah Ya na kin Mutum Mai yada alfasha"

Allah ya sa mu dace

*Shiek Lawal Abubakar Shuaib.*

(Hafizahullah)

Continue reading...

​​MUHIMMANCIN LOKACI A GURIN DAN ADAM

​​MUHIMMANCIN LOKACI A GURIN DAN ADAM 


​​LABARIN WANI BAKAUYE MAI YIN SUU DA MATARSA


​@ Wani bawan Allah ne yake rayuwa da matarsa a wani Kauye su biyu, Bashi da arziki wato talaka ne sosai kuma sana'arsa itace yin SUU, (wato kamo kifi).​


​@ Ranar nan ya tashi da safe matarsa take ce masa babu komai a gidan da zasu ci, shikenan yace mata bari yaje ya ga ko za'a samo wani abun. Ya dauki kayan SUU dinshi ya fita yaje yana kamo kifi, akayi rashin sa'a kifi 

 daya kawai samo a wannan rana, haka ya dawo gida ya bawa matar yace ta dafa musu shi su ci, tana cikin aikinsa sai ta ga wani abu mai sheki acikin kifi, ai kuwa sai ta sanar da mijinta. Da zuwansa sai yaga ashe Diamond ne suka tsinta acikin Kifin nan. Ai kuwa sai murna saboda kakarsu ta yanke saka.​


​@ Daga nan sai ya tafi cikin gari don ya sayar da wannan Diamond ko Gwal da suka tsinta acikin kifi shi da matarshi, duk inda yaje sai a rasa mai siya saboda kowa bashi da kudin da zai iya siyan wannan abu mai girma da daraja. Daga karshe aka kaishi gurin wani Attajiri wanda yafi kowa kudi a garin, shi ma dai yace masa bazai iya siya ba, sai dai a kaiwa sarki ko zai iya siya.​


​@ A kaje fada, aka nunawa Sarki, shima sarki yace ba zai iya biyan kudin wannan Diamond din ba ko Gwal, sai dai akwai wani daki na ajiya da ake ajiye duk wata dukiya ko kyauta ta Masarautar tun iyaye da 'ka'kanni kuma ba'a taba dauka ba, kullin dakin a rufe yake sai dai azuba a rufe. Sarki yace za'a bude maka wannan dakin ka shiga na tsawon awa 6 ka shiga ka dibi duk abinda yayi maka, amma sharadin shine idan awa Shida 6 tayi, zaka fito. Malam mai SUU yace ya yarda.​


​@ Mutumin ya shiga, shigarsa ke da yiwa, sai yaga wani lafiyayyen gado ga abinci kala kala an ajiye a gefen gadon, ai kuwa sai ya zauna yaci ya koshi, sai yace bari ya dan kwanta ya huta na tsawon minti 30 zuwa awa 1. 

Idan ya tashi ai yana da sauran awa 5 da zai Debi duk abin da yake so. Ai kuwa kwanciyarsa ke da yiwa sai bacci ya kwashe shi, bai tashi farkawa ba sai ji yayi ana buga masa kofa ana cewa Lokaci yayi ya fito, sai ya tashi a firgice yana rokon a taimaka masa koda minti 1 ne a bashi don ya dauki ko da abu daya ne, amma ina fadawa suka ce A'a, ai ba haka akayi dashi ba...... 

 haka ya fito bai dauki komai ba, yayi asarar Diamond dinsa kuma yayi asara bai fito da komai ba daga dakin ajiya .



            ​@ DARASI @


​@ Wannan Gwal ko Diamond da mutumin nan ya samu shine matsayin ​RAYUWA​​


​@ Wannan Dakin da ya shiga shine matsayin ​DUNIYA 


​ Wannan Kayan alato da gado da kayan mure rayuwa da ya gani sune ​KYALE KYALEN DUNIYA ​​


​@ Wannan Awa shida (6) da aka bashi shine ​ADADIN LOKACIN SA DUNIYA​ wanda ya nemi A kara masa koda minti 1 amma aka ce masa sam babu wannan zancen, to haka idan kazo mutuwa babu karin lokaci Allah yace:​ ​فإذا جاء أجلهم لا يستأخرون ساعة​


​@ wannan mutanen kuwa da suka zo fitar dashi daga wannan dakin sune ​MALA'IKU​​


​ @Kwankwasa kofa da yaji ana yi masa wannan ​MUTUWA CE​​

Continue reading...

SIHIRUL MAHABBA

MA'ANAR SIHIRUL MAHABBA:-

       Wani nau'i ne na sihiri da ake yi domin soyayya a :-

   1)- Saka soyayya tsakanin mutane guda biyu,misali tsakanin namiji da mace.

   2)- Saka soyayya tsakanin mutane da wasu abubuwa dabam wadanda ba mutane ba,

 

GAMAMMUN ALAMOMIN SIHIRI

   1)- Yawan ciwon kai 

   2)- Yawan ciwon mara(mafi yawancii bayan sallar la'asar ko cikin dare)

   3)- Yawan Yin Munanan Mafarkai(Kamar macizai,namun daji)

 

 

ALAMOMIN SIHIRIN MAHABBA(YAYA ZA'A GANE SIHIRUL MAHABBA)   

      1)- Tsananin soyayya,wadda ta faru kwatsam,wato asali ba soyayya tsakanin mutum ko mutane sai a ga sun fara soyayya,(Yana da kyau a ban-bance soyayya ta dan adam,)

      

      2)- Tsananin son saduwa zuwa ga abokin auraatayya(Wannan zai iya faruwa a dabi'ance sai dai sauran alamomi ne zasu banbance)

 

    3)- Gajen Haquri na rashin ganin masoyi/ya.

 

   4)- Yawan Mafarke mafarke akan dayan masoyi,(wanda ya wuce ka'ida)

   5)- Tsananin Biyayya ga daya daga cikin masoya(mutum kan sabawa iyayensa/ta don biyayya gareta/shi)

   6)- Tsananin kishi akansa/ta(Wanda hakan kansa mutum bazai iya nisantar ta/shi ba)

    

 

MATSALOLIN DA KAN AFKU WAJEN HADA SIHIRIN DAGA WURIN                                                     BOKA 

 

     1)- Zai iya juyawa zuwa ga tsananin kiyayya idan bokan yayi kuskuren hadawa.

     2)-Yakan shiga da karfi wanda hakan yakan sawa wanda akayiwa cuta ko ma ya karshi(domin wannan sihiri yakan canza zuciya daga kiyayya zuwa soyayya ne cikin kankanen lokaci)

    3)- Yakan juye zuwa son ko wane namiji/mace(mutum yaso ko wace mace har mahaifiyarsa/namiji har mahaifinta)

 

     HANYOYIN KARYA SIHIRUL MAHABBA

 

1- GAMAMMUN HANYOYI NA KARYA SIHIRUL MAHABBA

A)- Tsakake akida daga tsafi,layu ko guraye ,dolene mutum ya cire duk wani guri ko laya dake tare dashi.

B)- Mutum ya fahimci cewar duk abinda ya faru a gareshi daga Allah(SWT) ne da izninsa ya faru kuma yaso hakan ya faru shiyasa ya faru, Fadin Allah Q 2 Ch 102

C)- Kawar da duk wasu hotuna daga jikin bangon daki da kuma duk wani abu da yake da sura a jikinsa kamar posta d.s

D)- Dolene mace idan wanda zaiyi mata Ruqya Namijine ta sutuce jikinta da kaya masu rufe jiki gaba daya.

E)- Haqikance Labarin wanda abin ya afku akansa domin fara magani.

 

2)- HANYOYIN KARYA SIHIRUL MAHABBA ZABABBUN HANYOYI

RUQA

KAMAR HAKA:-

  KARANTA AL'QURANI MAI GIRMA

KA'IDA:

    A)- Dolene mutum wanda zaiyi ya kasance yana da tsarki kafin ya fara

    B)- Dukkan wadanda zasu kasance a gurin yana da kyau su kasance cikin tsarki saboda kar shi aljanin ya fita ya shiga jikin daya daga cikin mahalartan.

   C)- Allah ne ke bayar da Lafiya ba mai karatun ba.

GABA DAYAN AL'QURANI KARIYA NE , Amma wadannan suna daga cikin surori da Ayoyin da aka fiya amfani dasu:-

a)- Suratul Baqara : Ayata 1-4,Aya 102,Ayata 164,Ayata 256, Ayata 285-286.

b)- Suratul Al-imran :- Ayata 17-18.

c)- Suratul A'araf :54-56, Ayata 117-122(ana maimaita wadannan ayoyi)

d)- Suratul Yunus :- Ayata 80-82(Ana maimaita wannan aya)

e)- Suratul Mu'uminun :- Ayata 115-118

f)- Suratul Saffat :- Ayata 1-10

g)-Suratul Daha :- Ayata 69(Ana maimaita wannan aya)

h)- Suratul sajadah: Gaba dayanta

i)- Suratul Ahqaf :- Ayata 29-32

j)- Suratu:- Rahman :Ayata 33-36

h)- Suratu Hashar :- Ayata 21-24

k)- Suratul Jinn :Ayata 1-9

l)- Suratul Nas,Falaq,Ikhlas.

 

WASU KA'IDOJI YAYIN KARATUN

1- Mai yin karatun zaisa Hannunsa akan goshin maras lapiyan,ko kuma ya riqe jijiyoyin hannunsa don kada aljanun su gudu.

2-Idan Kuna cikin yin RUQA sai shi maras lapiyan yafara qaqarin yin amai(Haraswa) to zaku tsaya da yin karatun ku karanta su wadannan ayoyin a cikin ruwa (za'a iya sa magarya a cikin ruwan) abawa maras lapiyar ya sha,Cikin Ikon Allah zai iya amayar da sihirin idan ya cine a cikin abinci/ko abin sha.

3-Idan kuma jikinsa yayi zafi matuqa sai a riqa shafa masa ruwan wannan addu'a wato ayoyin da aka karanta a cikin ruwan +/- Magarya.

4-Idan Aljanin yazo kuyi kokarin magana da shi kamar haka:

  @@ Ya ya sunanka/ki?

 @@ Addininka/ki

 @@ Yaya akayi ka shiga jikin ta/shi

@@ A ina aka binne sihirin d.s

5- Yana Da kyau mu fahimci cewar mafiyawancin aljanu suna da karya don haka ko da sun fadi sunan wani mutum cewar "wane ko wance ce/ne tayi ko yayi sihirin kada a dauki maganar sa ,ko rinjayar da maganar kawai akan inda aka binne sihirin don a toneshi domin karyashi.

 

YAYA ZA'AYI IDAN ALJANIN BAI FADI GURIN DA AKA BINNE SHI BA

1-Sai shi mai RUQA din da kuma Yan'uwan maras lapiyan su yanki wani lokaci cikin yini ko dare(hala ma kashi uku cikin dare) domin su roki Allah akan ya nuna musu gurin da aka binne wannan sihirin.

2-Yawan Karanta Aya 255, wato AYATUL KURSIYY Na kashe aljani da kuma tilasta musu fita daga jikin mutum.

 

WASU DOKOKI DA MUTUM ZAI KIYAYE BAYAN KARYA SIHIRIN

Haqiqa Yin Shiru wato kada mutum yayi ta fadi cewar an karya masa/ta sihiri na daga cikin abubuwan dake taimakawa ,domin fadiwa mutane zai iya kaiwa kunnen wanda yayi sihirin kuma zai iya Komawa ya sake maimaita wa.

1-Riko da sunnar Annabi(SAW)

2-Tsaftace abinci da abin sha(nema da cin halas)

3- Daina Jin kade-kade da wake-wake.

4-Daina sa matsatstsun kaya da kiyaye tsiraici.

5- Riko da Azkar na safiya da yamma.

6- Kwnaciya da Alwala.

7- Karanta Surori ko Ayoyin neman tsari a yayin kwanciya,

8-Nisantar Duk wasu hanyoyin sabon Allah(SWT)

9-Fara Cin Abinci da bismillah wannan kan karya sihiri idan an sakashi cikin abinci

10- Addu'oin fita da kuma shiga gida

11- Addu'oin Sa kaya ko kuma cre kaya

12- Addu'ar shiga bayan daki

 


 

Continue reading...

YADDA ZAKA GANE BOKA

GA YADDA BOKA KE TAMBAYARSA WAJEN SANIN CUTA:-

       1- Zai tambayi ka/ki sunan ki/ka da na mahaifiya(basa tambayar sunan mahaifi domin sihiri da sunan mahaifiya akeyinsa)


      2-Neman wani bangare na jikin mutum: kamar Gashin kai,Farce, Da sauransu


      3)- Neman wani Abu wanda ya taba jikin matumin da za ayi wa sihirin(Wato dole ne sai kayan da Gumi ko zufa(sweat) na mutumin ya taba kafin a wanke saboda haka yana da kyau mu lura da kayan da muke zubarwa ko kuma wasu suce mu basu kaya,) ,ko daukar sawun kafa na mutum wato kasar mutum ya taka ba takalmi,


     4-Nema akai masa wani bayyanannan abu kamar Farin goro,Jan zakara ko kaza,bakar akuya ko dan taure,ko kuma bangare na jikin wasu halittu,


    5-Sukan Nemi Da mutum yayi wani aiki wanda Allah Ya haramta (domin nemo fushin Allah) kamar sallah ba alwala, zina da wadanda aka haramtawa mutum kamar akanwa ko mahaifiya ko Yayar mutum ko kuma Yar'sa,


  6)- Rubutawa mutum Wani Hatimi ko bashi wasu tarin layu yasa a jikinsa da yi masa sharadin cewar "MATUQAR YA RABU DA ITA TO BAZAI SAMU KARIYA BA KO KUMA WANI ABU ZAI SAMESA"


  7- Wani lokaci zaka ji yana karatu maras ma'ana,ko kuma ya kawo kalamai marasa ma'ana a tsakiyar karatun Al-qur'ani kamar..."JIB YADAKA YANUS,JIB YA SAQARADDIN," Wato yana kiran sunayen wasu aljanu.


  8- Sukan Bayr da umarni ga mutum,ko kuma maras lapiyan da yaje gurinsu domin neman lapiya akan ya lazimci fadin wasu kalamai ko kuma ya yawaita  zuwa suna Sanennan guri yaana yin wani aiki da zasu Gindaya masa.


 

Continue reading...

DALILAN DA YASA SIHIRI DA MASU SIHIRI SUKA YAWAITA

DALILAN DA YASA SIHIRI DA MASU SIHIRI SUKA YAWAITA:-

 

    1- Karancin Ilmin sanin Haqiqanin Hukunci da tsananin uqubar da Allah SWT Ke yiwa masu sihiri,ko masu zuwa ayi musu  sihirin

 

  2- Son zuciya da son duniya da kale-kalen cikinta da Mantawa Da Ranar Alqiyama da rayuwar kabari.

  3- Yawaitar Bokaye Wadanda Suke saye da rigunan maluma,wato Mutane basa iya banbance haqiqanin boka da malamin sunnah, saboda jahilci.

 

 4- Neman mulki ta ko wace hali,ko kafa,

 

Continue reading...

MA'ANAR SIHIRI

MA'ANAR SIHIRI A HARSHEN LARABCI:-

 

  SIHIRI :-

      1)-Wani aiki ne wanda ake kusanta zuwaga shaidanu ta wadansu haramtattun hanyoyi,

      2)- Canza Abu daga ainahin yadda yake zuwa wata sifa da ban.

      3)- Juya wa daga lapiya zuwa cutarwa ta hanyar amfani da shaidanu



MA'ANAR SIHIRI A SHARI'AR MUSULINCI:

 

     SIHIRI:-

 

        1)- Wani aiki ne wanda ya kunshi duk wata cuta ko kuma canzawa daga lapiya zuwa jiya,tare da boyuwar dalilan da suka kawo cutar, kuma cikin kankanan lokaci tare da rudarwa da rikita tunanin wadanda abinya samesu,

 

       2)- Duk wata kalma ko kalamai wadanda wadanda wani zaiyi amfani dashi wajen sa cuta ko kuma illa ga jikin wani dan adam da ban,

Continue reading...

Addu'ar Bude Sallah (watau Bayan An yi Kabbarar Harama)

Addu'ar Bude Sallah (watau Bayan An yi Kabbarar Harama)


اَللَّهُـمَّ باعِـدْ بَيـنِي وَبَيْنَ خَطـايايَ كَما باعَدْتَ بَيْنَ المَشْرِقِ وَالمَغْرِبْ ، اَللَّهُـمَّ نَقِّنِـي مِنْ خَطايايَ كَمـا يُـنَقَّى الثَّـوْبُ الأَبْيَضُ مِنَ الدَّنَسْ ، اَللَّهُـمَّ اغْسِلْنِـي مِنْ خَطَايَـايَ بِالثَّلـجِ وَالمـاءِ وَالْبَرَدْ .

 Allahumma ba'id baynee wabayna khatayaya kama ba'adta baynal-mashriki walmaghrib, allahumma nakkinee min khatayaya kama yunakkath-thawbul-abyadu minad-danas, allahummagh-silnee min khatayaya biththalji walma'i walbarad.


Ya Allah! Ka nisanta tsakanina da laifuffukana kamar yadda Ka nisanta tsakanin gabas da yamma; Ya Allah! Ka tsarkake ni daga laifuffukana kamar yadda ake tsarkake farar tufa daga dauda, Ya Allah! Ka wanke ni daga laifuffukana da kankara da ruwa da raba.



سُبْـحانَكَ اللّهُـمَّ وَبِحَمْـدِكَ وَتَبارَكَ اسْمُـكَ وَتَعَـالَى جَـدُّكَ وَلا إِلهَ غَيْرُكَ.

Subhanakal-lahumma wabihamdika watabarakas-muka wata'ala jadduka wala ilaha ghayruk.


Tsarki ya tabbata gareKa, Ya Allah, tare da yabo gareka; Albarkatun sunanka sun yawaita; mulkinka da girmanka sun daukaka; babu abin bautawa da gaskiya ba Kai ba.


 

وَجَّهـْتُ وَجْهِـيَ لِلَّذِي فَطَرَ السَّمـَوَاتِ وَالأَرْضَ حَنِـيفَاً وَمَـا أَنَا مِنَ المشْرِكِينَ، إِنَّ صَلاَتِـي، وَنُسُكِي، وَمَحْـيَايَ ، وَمَمَاتِـي ِللهِ رَبِّ العالَمِينَ، لاَ شَرِيـكَ لَهُ وَبِذَلِكَ أُمِرْتُ وَأَنَا مِنَ الْمُسْلِـمِينَ. اَللَّهُـمَّ أَنْتَ المَلِكُ لاَ إِلهَ إِلاَّ أَنْتَ ،أَنْتَ رَبِّـي وَأَنَـا عَبْـدُكَ ، ظَلَمْـتُ نَفْسِـي وَاعْـتَرَفْتُ بِذَنْبِـي فَاغْفِرْ لِي ذُنُوبِي جَمِيعاً إِنَّـهُ لاَ يَغْـفِرُ الذُّنـُوبَ إلاّ أَنْتَ .وَاهْدِنـِي لأَحْسَنِ الأَخْلاقِ لاَ يَهْـدِي لأَحْسَـنِهَا إِلاَّ أَنْـتَ، وَاصْـرِفْ عَـنِّي سَيِّئَهَـا، لاَ يَصْرِفُ عَـنِْي سَيِّئَهَـا إِلاَّ أَنْـتَ، لَبَّـيْكَ وَسَعْـدَيْكَ، وَالْخَـيْرُ كُلُّـهُ بِيَـدَيْـكَ، وَالشَّرُّ لَيْـسَ إِلَـيْكَ، أَنَا بِكَ وَإِلَيْـكَ، تَبَـارَكْتَ وَتَعَـالَيتَ أَسْتَغْـفِرُكَ وَأَتُوبُ إِلَـيْكَ.

Wajjahtu wajhiya lillazee fataras-samawati wal-arda haneefan wama ana minal-mushrikeen, inna salatee wanusukee wamahyaya wamamatee lillahi rabbil-'alameen, la shareeka lahu wabithalika umirtu wa-ana minal-muslimeen. Allahumma antal-maliku la ilaha illa ant. anta rabbee wa-ana 'abduk, zalamtu nafsee wa'taraftu bizanbee faghfir lee thunoobee jamee'an innahu la yaghfiruz-zunooba illa ant.wahdinee li-ahsanil-akhlaki la yahdee li-ahsaniha illa ant, wasrif 'annee sayyi-aha la yasrifu 'annee sayyi-aha illa ant, labbayka wasa'dayk,walkhayru kulluhu biyadayk, washsharru laysa ilayk, ana bika wa-ilayk, tabarakta wata'alayt, astaghfiruka wa-atoobu ilayka.


Na juya fuskata ga wanda ya kagi halittar sammai da kassai, ina mai karkata ga addini na gaskiya, kuma ni ba na cikin mushrikai. Lallai sallata da ayyukan ibadata da rayuwata da mutuwata na Allah ne, Ubangijin talikai; babu abokin tarayya a gare Shi, kuma da wannan aka umarce ni, kuma ni ina daga Cikin Musulmi. Ya Allah! Kai ne Sarki, babu abin bautawa da gaskiya sai Kai; kai ne Ubangijina, kuma ni bawanka ne, na zalunci kaina, kuma na tabbata da zunubina; Ka gafarta mini zunubaina dukkanninsu, ba wanda yake gafarta zunubai sai Kai; Ka gusar da miyagunsu daga gare ni, babu wanda zai gusar da miyagunsu daga gareni sai Kai. Amsa maka, da biyayya gare ka bayan biyayya; kuma arziki naka ne, kuma alherin dukkaninsa yana hannunka, sharri kuma ba a danganta shi gare Ka. Ni kuma dacewata tana gare Ka, kuma gare Ka nake fakewa. Alherinka ya yawaita, kuma Ka daukaka. Ina neman gafarrka, kuma ina tuba gare Ka.



اللّهُـمَّ رَبَّ جِـبْرَائِيلَ، وَمِيكَـائِيلَ، وَإِسْـرَافِيلَ، فَاطِرَ السَّمَوَاتِ وَالأَرْضِ، عَالِمَ الغَيْبِ وَالشَّهَادَةِ أَنْتَ تَحْكُمُ بَيْـنَ عِبَادِكَ فِيمَا كَانُوا فيهِ يَخْتَلِفُونَ. اهْدِنِي لِمَا اخْتُلِفَ فِيهِ مِنَ الْحَقِّ  بِإِذْنِكَ، إِنَّـكَ تَهْـدِي مَنْ تَشَـاءُ إِلَى صِرَاطٍ مُسْتَقَيمٍ.

Allahumma rabba jibra-eel, wameeka-eel, wa-israfeel fatiras-samawati walard, 'alimal-ghaybi washshahadah, anta tahkumu bayna 'ibadika feema kanoo feehi yakhtalifoon. ihdinee limakh-tulifa feehi minal-haqqi bi-ithnik, innaka tahdee man tasha-u ila siratin mustaqeem.


Ya Allah! Ya Ubangijin Jibrilu da Mika'ilu da Israfilu! Mai kagen halittar sammai da kassai, masanin fake da sarari! Kai ne Kake hukunci tsakanin bayinka Cikin abin da suka kasance suna sassabawa a cikinsa (na gaskiya). Ka shirye ni zuwa ga abin da aka sassaba a cikinsa na gaskiya da Nufinka; hakika Kai ne mai shiryar da wanda Ka so (shiriyarsa) zuwa ga tafarki madaidaici.



اللهُ أَكْبَرُ كَبِيرًا، اَللهُ أَكْبَـرُ كَبِيرًا، اللهُ أَكْبَـرُ كَبِيرًا، وَالْحَمْدُ للهِ كَثيرًا، وَالْحَمْدُ للهِ كَثِيرًا، وَالْحَمْدُ للهِ كَثِيرًا، وَسُبْـحانَ اللهِ بكْـرَةً وَأَصِيلاً. (ثَلاَثاً)

أَعُـوذُ بِاللهِ مِنَ الشَّـيْطَانِ مِنْ نَفْخِـهِ وَنَفْـثِهِ وَهَمْزِه .

Allahu akbaru kabeera, Allahu akbaru kabeera, Allahu akbaru kabeera, walhamdu lillahi katheera, walhamdu lillahi katheera, walhamdu lillahi katheera, wasubhanal-lahi bukratan wa-aseela. (3)


A'uthu billahi minash-shaytani min nafkhihi wanafthihi wahamzih.


Ina girmama Allah girmamawa, ina girmama Allah girmamawa, ina girmama Allah girmammawa. Kuma yabo ya tabbata ga Allah, a safiya da yammaci (sau uku). Ina neman tsari da Allah daga shaidan, daga hurawarsa, da tofinsa da kuma zungure-zungurensa.



Annabi, tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi, ya kasance idan ya tashi Cikin dare zai yi sallar dare (tahajjudi) yana cewa;

َاللّهُمَّ لَكَ الْحَمْدُ أَنْتَ  نُورُ السَّمَـوَاتِ وَالأَرْضِ وَمَنْ فِيـهِنَّ، وَلَكَ الْحَمْدُ أَنْتَ قَـيِّمُ السَّـمَوَاتِ وَالأَرْضِ  وَمَنْ فيـهِن، [وَلَكَ الْحَمْدُ أَنْتَ رَبُّ السَّـمَوَاتِ وَالأَرْضِ  وَمَنْ فِيـهِنَّ] [وَلَكَ الْحَمْدُ لَكَ مُلْـكُ السَّـمَوَاتِ وَالأَرْضِ  وَمَنْ فِيـهِنَّ]   [وَلَكَ الْحَمْدُ أَنْتَ مَلِـكُ السَّـمَوَاتِ وَالأَرْضِ] [وَلَكَ الْحَمْدُ] [أَنْتَ الْحَقُّ وَوَعْـدُكَ الْحَـقُّ، وَقَوْلُـكَ الْحَـقُّ، وَلِقَاؤُكَ الْحَـقُّ، وَالْجَـنَّةُحَـقٌّ، وَالنّـارُ حَـقٌّ، وَالنَّبِـيُّونَ حَـقٌّ، وَمُـحَمَّدٌ  حَـقٌّ، وَالسّـاعَةُحَـقٌّ]  [اللّهُـمَّ لَكَ أَسْلَمْتُ، وَعَلَـيْكَ تَوَكَّلْـتُ، وَبِكَ آمَنْـتُ، وَإِلَـيْكَ أَنَبْـتُ ، وَبِـكَ خَاصَمْتُ، وَإِلَـيْكَ حاكَمْـتُ. فَاغْفِـرْ لِي مَـا قَدَّمْتُ ، وَمَا أَخَّـرْتُ، وَما أَسْـرَرْتُ، وَمَا أَعْلَنْتُ]  [أَنْتَ الْمُقَـدِّمُ وَأَنْتَ المُـؤَخِّرُ، لاَ إِاَـهَ إِلاَّ أَنْـتَ]  [أَنْـتَ إِلَهِي لاَ إِلَهَ إِلاَّ أَنْتَ.

Allahumma lakal-hamd anta noorus-samawati wal-ardi waman feehin, walakal-hamd, anta kayyimus-samawati walardi waman feehin, [walakal-hamd, anta rabbus-samawati walardi waman feehin], [walakal-hamd, laka mulkus-samawati walardi waman feehin] [walakal-hamd, anta malikus-samawati walard] [walakal-hamd] [antal-haq, wawaAAdukal-haq, wakawlukal-haq, walika-okal-haq, waljannatu haq wannaru haq, wannabiyyoona haq, wa Muhammadun  haq, wassaAAatu haq] [allahumma laka aslamt, waAAalayka tawakkalt, wabika amant, wa-ilayka anabt, wabika khasamt, wa-ilayka hakamt, faghfir lee ma kaddamt, wama akhkhart, wama asrart, wama a'lant] [antal-mukaddim, wa-antal-mu-akhkhir, la ilaha illa ant] [anta ilahee la ilaha illa anat .


Ya Allah! Dukkan yabo ya tabbata gare Ka, Kai ne hasken sammai da kassai da wanda ke cikinsu; kuma dukkan yabo ya tabbata gare Ka, Kai ne mai tsayar da sammai da kassai da wanda ke cikinsu da karfin ikonka; kuma dukkan yabo ya tabbata gare Ka, Kai ne Ubangijin sammai da kassai da wanda ke cikinsu; kuma dukkan yabo ya tabbata gare Ka, Kai ne gaskiya, kuma alkawarinka shi ne gaskiya, kuma maganarka ita ce gaskiya, kuma saduwa da Kai ita ce gaskiya, kuma aljanna gaskiya ce, wuta ma gaskiya ce, Annabawa ma gaskiya ne, (Annabi) Muhammadu ma, tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi, gaskiya ne, sa'ar kiyama ma gaskiya ce. Ya Allah! Gare Ka kadai na mika wuya, kuma da Kai kadai na dogara, kuma da Kai kadai na yi imani, kuma zuwa gare Ka kadai nake komawa, kuma saboda Kai ne kadai na yi jayayya, kuma gare Ka kadai na kai hukunci. Don haka Ka gafarta mini abin day a wuce da abin da zai zo da abin da na boye da abin da na bayyana, Kai ne mai gabatarwa, kuma Kai ne mai jinkirtawa, babu abin bautawa da gaskiya sai Kai. Kai ne wanda nake bautawa; babu abin bautawa da gaskiya sai Kai.


Continue reading...

Addu’a yayin kiran Sallah - Hisnul Muslim

Addu’a yayin kiran Sallah :

Wanda ya ji kiran sallah zai fadi dukkan abin da ladanin yake fadi, sai dai idan yace;

حَيَّ عَلَى الصَّلاَةِ، حَيَّ عَلَى الْفَلاَحِ.

Hayya Alas Salah, Hayya Alal Falah.

Ku taho ga Sallah, ku taho ga babban rabo.


Maimakon haka sai shi ya ce:

لا حَـوْلَ وَلا قُـوَّةَ إِلاّ بِالله.

La hawla wala kuwwata illa billah.


Babu daraba, babu karfi sai da Allah.


وَأَنا أَشْـهَدُ أَنْ لاَ إِلَـهَ إِلاّ اللهُ وَحْـدَهُ لاَ شَـريكَ لَـهُ، وَأَنَّ محَمّـداً عَبْـدُهُ وَرَسُـولُهُ ، رَضِيـتُ بِاللهِ رَبَّاً ، وَبِمُحَمَّـدٍ رَسُـولاً وَبِالإِسْلامِ دِينًا .

Wa-ana ashhadu an la ilaha illal-lahu wahdahu la shareeka lah, wa-anna Muhammadan AAabduhu warasooluh, radeetu billahi rabban wabimuhammadin rasoolan wabil-islami deena.


Ni ina shaidawa cewa babu abin bautawa da gaskiya sai Allah, shi kadai, babu abokin tarayya a gare Shi. Kuma Allah shi ne Ubangiji, kuma Muhammadu shi ne Manzo, kuma Musulunci shi ne addini.



Bayan ya gama amsa kiran sallar, sai ya yi salati ga Annabi, tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi.


Sannan ya ce:

اللّهُـمَّ رَبَّ هَذِهِ الدّعْـوَةِ التّـامَّةِ وَالصّلاةِ القَـائِمَة آتِ محَـمَّداً الوَسيـلةَ وَالْفَضـيلَة وَابْعَـثْهُ مَقـامًـا مَحْـمُوداً الَّذِي وَعَـدْتَهُ إِنَّـكَ لا تُـخْلِفُ الْمِيـعَادَ.

 Allahumma rabba hathihid-da'watit-tammah, wassalatil-ka-imah ati Muhammadan alwaseelata wal-fadeelah, waba'ath-hu makaman mahmoodan allazee wa'adtahu, innaka la tukhliful-mee'ad.


Ya Allah! Ubangijin wannan kira kammalalle, da wannan sallar da za a tsayar da ita. Ka ba wa Muhammadu wasila (matsayin kusanci a cikin Aljanna), da matsayin fifiko, kuma ka tashe mu a matsayi abin godewa, wannan wanda Ka yi masa alkawarinsa. Lallai kai ba ka saba alkawari.



Sannan ya yiwa kansa addu'a tsakanin kiran sallah da tayar da ikama, domin addu'a a wannan lokaci ba a kin karbarta.


Continue reading...

HUKUNCE-HUKUNCEN MAI TAKABA

*_HUKUNCE-HUKUNCEN MAI TAKABA_*

*Tambaya:*

Assalamu alaikum wa rahmatullaah. gafarta Malam pls ayi mana bayani koda a takaice ne dangane da hukunce - hukuncen takaba... Na shiga wajen mahaifiya dazu, take cewa in tambaya mata Malamai tanadin shari'a akan wannan al'amari. Nagode

*Amsa:*

Wa'alaikum assalam To dan'uwa ina rokon Allah ya jikan mahafinku, akwai hukunce-hukunce da suka shafi takaba, ga muhimmai daga ciki:

*1.* Mai takaba za ta zauna a gidan mijinta ba za ta fita ba, har sai ta gama iddarta, wacce take wata hudu da kwana goma, kamar yadda aya ta: 234 a suratul Bakara take nuni zuwa hakan .

*2.* Ba za ta saka kaya masu kyau ba, don haka za ta guji ado, kamar yadda hadisin Abu-dawud mai lamba ta: 2304, ya yi bayanin hakan.

*3.* Shari'a ta hana mai takaba ta sanya turare, kamar yadda hadisin Bukhari mai lamba ta: 5343, ya tabbatar da hakan,

*4.* Malamai suna cewa mai takaba ba za ta sanya tozali ba, kamar yadda hadisin Nasa'i mai lamba ta: 3565 ya bayyana hakan.

*5.* An hana mai takaba yin lalle, kamar yadda hanin ya zo a hadisin Abu-dawud mai lamba ta: 2304.

*6.* Idan wata bukata ta kama za ta iya fita daga gida, ko da rana ne ko da dare.

*7.* Za ta iya yin Magana da mazan da ba muharramanta ba, idan bukatar hakan ta kama, saidai ta guji, sanyaya murya, kamar yadda aya ta 32 a suratul-ahzab ta hana sanyaya murya ga wadanda ba muharramai ba.

*8.* Babu wani launi na kaya na musamman da aka shar'anta mata ta sanya, don haka, duk kayan da ba kwalliya a jikinsu ya halatta ta sanya su .

*9.* Za ta iya yin wanka da sabulun da yake ba mai kanshi ba.

*10.* Za ta iya zama ta yi hira da makusantanta, har ma za ta iya bude gashin kanta, idan su duka muharramanta ne.

*11.* Bai halatta wani ya nemi auranta ba, har sai ta gama idda, saidai za'a iya yin jirwaye mai kama da wanka, kamar yadda aya ta 235 ta yi nuni zuwa hakan.

*12.* Idan mai takaba tana da ciki, to iddarta ita ce: haife abin da take dauke da shi, kamar yadda hadisin Subai'a mai lamba ta: 5014 a Sahihul Bukhari ya tabbatar da hakan.

Allah ne mafi sani.

27\3\2015

Amsawa:-Dr. Jamilu Zarewa.

Continue reading...

BA A BARIN YIN AIKI DA INGANTATTUN HADITHAI SABODA KAWAI SUN SABA WA MAGANAR WANI KO AIKINSA


Wajibi ne a kan Musulumi ya gina addininsa a kan

sunnar Annabi mai tsira da amincin Allah; saboda

duk wanda ya bar yin aiki da ingantaccen hadithin

Annabi mai tsira da amincin Allah cikin wata

mas'ala cikin mas'aloli, cikin zabinsa da jin dadinsa

a bisa hujjar cewa: mazhabarsa ta saba wa hadithin,

ko wata darika tasa ta Sufaye ta saba wa hadithin,

ko wani tsari na kungiyarsa ya saba wa hadithin, ko

wani tsari na duniyarsa ya saba wa hadithin to lalle

wannan ya bace ya bar hanyar Muminai. Wannan shi

ne abin da nassoshin Alkur'ani mai girma da Sunnah

mai daraja ke tabbatarwa. Shaikhul Islam Ibnu

Taimiyah ya ce cikin Majmuu'ul Fataawaa 24/202:-

(( ﻭﺍﻣﺎ ﻣﻦ ﺗﺒﻴﻨﺖ ﻟﻪ ﺍﻟﺴﻨﺔ ﻓﻈﻦ ﺍﻥ ﻏﻴﺮﻫﺎ ﺧﻴﺮ ﻣﻨﻬﺎ ﻓﻬﻮ ﺿﺎﻝ

ﻣﺒﺘﺪﻉ ﺑﻞ ﻛﺎﻓﺮ )).

Ma'ana: ((Amma wannan da Sunnah ta bayyana gare

shi, sannan ya yi zaton cewa waninta ya fi ta alheri,

to shi dan'bidi'ah ne, kai kafiri ne ma)).

Ya kuma ce cikin littafin 27/125:-

(( ﻭﻣﻦ ﺗﺮﻙ ﺍﻟﻨﻘﻞ ﺍﻟﻤﺼﺪﻕ ﻋﻦ ﺍﻟﻘﺎﺋﻞ ﺍﻟﻤﻌﺼﻮﻡ ﻭﺍﺗﺒﻊ ﻧﻘﻼ ﻏﻴﺮ

ﻣﺼﺪﻕ ﻋﻦ ﻗﺎﺋﻞ ﻏﻴﺮ ﻣﻌﺼﻮﻡ ﻓﻘﺪ ﺿﻞ ﺿﻼﻻ ﺑﻌﻴﺪﺍ )).

Ma'ana: ((Wanda ya bar nakalin da aka gaskata

daga mai fada wanda yake ma'asuu'mi, sannan ya

bi nakalin da ba a gaskata ba daga mai fadan da

ba ma'asuu'mi ba, hakika ya bace bata mai nisa)).

Allah Ya tausaya wa al'ummarmu ya cusa musu

ganin girman Annabi mai tsira da amincin Allah

cikin zukatansu, da kuma kaunar gabatar da

maganarsa a kan maganar waninsa cikin halittu.

Ameen.

Dr. Ibrahim Jalo Jalingo.

Continue reading...

MAULIDI A MAHANGAR MUSULUNCI

kamar yadda aka sani ne cewa wannan rana ta 12/3/

ita ce ranar da wasu ke bukin ranar haifuwar Annabi

Muhammad mai tsira da amincin Allah, saboda neman lada da

falala a wurin Allah, duk kuwa da cewa rikon wannan rana a

matsayin Idi bidi’a ce wurin dukkan Maluman Musulunci!

Haka dai Shaidan yake batar da mutane ta hanyar kawata musu

wani abin da ba Shari’ah ba ne har su rika ganin shi tamkar

abin da yake Shari’ah ne! Allah yana cewa cikin Suratu

Faatir aya ta 8:-

(( ﺃﻓﻤﻦ ﺯﻳﻦ ﻟﻪ ﺳﻮﺀ ﻋﻤﻠﻪ ﻓﺮﺍﻩ ﺣﺴﻨﺎ ﻓﺎﻥ ﺍﻟﻠﻪ ﻳﻀﻞ ﻣﻦ ﻳﺸﺎﺀ ﻭﻳﻬﺪﻱ

ﻣﻦ ﻳﺸﺎﺀ ﻓﻼ ﺗﺬﻫﺐ ﻧﻔﺴﻚ ﻋﻠﻴﻬﻢ ﺣﺴﺮﺍﺕ ﺍﻥ ﺍﻟﻠﻪ ﻋﻠﻴﻢ ﺑﻤﺎ

ﻳﺼﻨﻌﻮﻥ)).

Ma’ana: ((yanzu wanda aka kawata masa mummunan aikinsa

har ya gan shi wani abu Mai kyau “yana daidai da

waninsa?” saboda haka lalle Allah yana batar da wanda yake

so, kuma ya shiryar da wanda yake so, kada ranka ya halaka

a kansu saboda bakin ciki. Lalle Allah Masani ne ga abin da

suke sana’antawa)).

Mu a nan, a bisa dogara da ayah ta 104 a cikin Suratu Aali

inda Allah Ya ce:-

(( ﻭﻟﺘﻜﻦ ﻣﻨﻜﻢ ﺃﻣﺔ ﻳﺪﻋﻮﻥ ﺍﻟﻰ ﺍﻟﺨﻴﺮ ﻭﻳﺄﻣﺮﻭﻥ ﺑﺎﻟﻤﻌﺮﻭﻑ ﻭﻳﻨﻬﻮﻥ ﻋﻦ

ﺍﻟﻤﻨﻜﺮ ﻭﺃﻭﻟﺌﻚ ﻫﻢ ﺍﻟﻤﻔﻠﺤﻮﻥ )).

Ma’ana: ((A samu wata al’umma daga cikinku da za ta

yi kira zuwa ga alheri, sannan ta umurni da abin da

Shari’ah ta sani, kuma ta yi hani ga abin da Shari’ah bata

sani ba.

To su wadannan Al’umma sune masu rabauta)). Da

kuma dogara kan aya ta 78, da 79 cikin Suratul Maa’idah

inda Allah Madaukaki ya yi maga a kan Banuu Isaraa’iil ya

ce:-

(( ﻟﻌﻦ ﺍﻟﺬﻳﻦ ﻛﻔﺮﻭﺍ ﻣﻦ ﺑﻨﻲ ﺍﺳﺮﺍﺋﻴﻞ ﻋﻠﻰ ﻟﺴﺎﻥ ﺩﺍﻭﺩ ﻭﻋﻴﺴﻰ ﺍﺑﻦ

ﻣﺮﻳﻢ ﺫﻟﻚ ﺑﻤﺎ ﻋﺼﻮﺍ ﻭﻛﺎﻧﻮﺍ ﻳﻌﺘﺪﻭﻥ . ﻛﺎﻧﻮﺍ ﻻ ﻳﺘﻨﺎﻫﻮﻥ ﻋﻦ ﻣﻨﻜﺮ ﻓﻌﻠﻮﻩ

ﻟﺒﺌﺲ ﻣﺎ ﻛﺎﻧﻮﺍ ﻳﻔﻌﻠﻮﻥ )).

Ma’ana: ((An la’anci wadanda suka kafirta daga Banu

Isaa’iil a bisa harshen Daawuuda da Isa Dan Maryam, saboda

irin yadda suka yi sabo, suka kasance suna ketare iyaka. Suka

kasance ba sa hana juna yin mummunan aikin da suke

aikatawa. Wallahi abin da suka kasance suna aikatawa ya yi

muni)). Da kuma dogara kan hadithin da Imam Muslim ya

ruwaito hadithi na 49 inda Annabi mai tsira da amincin Allah

yake cewa:-

(( ﻣﻦ ﺭﺃﻯ ﻣﻨﻜﻢ ﻣﻨﻜﺮﺍ ﻓﻠﻴﻐﻴﺮﻩ ﺑﻴﺪﻩ ﻓﺎﻥ ﻟﻢ ﻳﺴﺘﻄﻊ ﻓﺒﻠﺴﺎﻧﻪ ﻓﺎﻥ ﻟﻢ

ﻳﺴﺘﻄﻊ ﻓﺒﻘﻠﺒﻪ ﻭﺫﻟﻚ ﺍﺿﻌﻒ ﺍﻻﻳﻤﺎﻥ )).

Ma’ana: ((Wanda duk ya ga munkari daga cikinku sai ya

jirkita shi da hannunsa, in kuma ba zai iya ba, sai ya jirkita

shi da harshensa, in kuma ba zai iya ba sai ya jirkita shi da

zuciyarsa, wannan shi ne mafi raunin Imani)). Da kuma

dogara kan maganar Sahabin Annabi Abdullahi Dan Mas’ud

Allah ya kara masa yarda, wacce ta zo cikin littafin Ibnu

Wadh,dhah shafi na 11 da littafin Ali’itisaam na Imamush

Shaatibii 1/107 inda ya ce:-

(( ﺍﺗﺒﻌﻮﺍ ﻭﻻ ﺗﺒﺘﺪﻋﻮﺍ ﻓﻘﺪ ﻛﻔﻴﺘﻢ )).

Ma’ana: ((Ku bi -abin da Annabi ya zo da shi- kada ku

kirkiri bidi’ah, domin an gama muku kome -na addini-)).

Dankuma dogara har yanzu a kan maganar shi Sahabi Abdullahi

Dan Mas’uud wacce ta zo cikin littafin Ibnu Wadh’dhah

shafi na 11 da kuma Sunanud Daarami 1/68-69 a inda ya ce

lokacin da ya wuce wani mai wa’azi a cikin masallaci yana

ce wa mutane: ku yi Subhanallah kafa goma, ku yi la’laha

illalah kafa goma, sai ya ce da su:-

(( ﻭﻳﺤﻜﻢ ﻳﺎ ﺃﻣﺔ ﻣﺤﻤﺪ ﻣﺎ ﺍﺳﺮﻉ ﻫﻠﻜﺘﻜﻢ ! ﻫﺆﻻﺀ ﺻﺤﺎﺑﺔ ﻧﺒﻴﻜﻢ ﺻﻠﻰ

ﺍﻟﻠﻪ ﻋﻠﻴﻪ ﻭﺳﻠﻢ ﻣﺘﻮﺍﻓﺮﻭﻥ ﻭﻫﺬﻩ ﺛﻴﺎﺑﻪ ﻟﻢ ﺗﺒﻞ ﻭﺃﺗﻴﺘﻪ ﻟﻢ ﺗﻜﺴﺮ ﻭﺍﻟﺬﻱ

ﻧﻔﺴﻲ ﺑﻴﺪﻩ ﺍﻧﻜﻢ ﻟﻌﻠﻰ ﻣﻠﺔ ﻫﻲ ﺃﻫﺪﻯ ﻣﻦ ﻣﻠﺔ ﻣﺤﻤﺪ ﺍﻭ ﻣﻔﺘﺘﺤﻮﺍ ﺑﺎﺏ

ﺿﻼﻟﺔ . ﻗﺎﻟﻮﺍ ﻳﺎ ﺃﺑﺎ ﻋﺒﺪ ﺍﻟﺮﺣﻤﻦ ﻣﺎ ﺍﺭﺩﻧﺎ ﺍﻻ ﺍﻟﺨﻴﺮ ﻗﺎﻝ ﻭﻛﻢ ﻣﺮﻳﺪ

ﻟﻠﺨﻴﺮ ﻟﻦ ﻳﺼﻴﺒﻪ ﺍﻥ ﺭﺳﻮﻝ ﺍﻟﻠﻪ ﺻﻠﻰ ﺍﻟﻠﻪ ﻋﻠﻴﻪ ﻭﺳﻠﻢ ﺣﺪﺛﻨﺎ ﺍﻥ ﻗﻮﻣﺎ

ﻳﻘﺮﺀﻭﻥ ﺍﻟﻘﺮﺍﻥ ﻻ ﻳﺠﺎﻭﺯ ﺗﺮﺍﻗﻴﻬﻢ ﻭﺍﻳﻢ ﺍﻟﻠﻪ ﻣﺎ ﺍﺩﺭﻱ ﻟﻌﻞ ﺍﻛﺜﺮﻫﻢ ﻣﻨﻜﻢ

ﺛﻢ ﻭﻟﻰ ﻋﻨﻬﻢ )).

Ma’ana: ((kaitonku ya ku al’ummar Muhammad mamakin

saurin halakarku! Wadannan Sahabban annabinku ne mai tsira da

amincin Allah ga su nan da yawa, wadannan tufafinsa ne ba

su gama yagewa ba, wadannan butocinsa ne ba su gama

fashewa ba. Ina rantsuwa da Wanda raina yake hannunsa lalle

ne ku ko dai kuna kan wani addini ne da ya fi addinin

Muhammad shiriya ko kuwa ku masu bude kofar bata ne. Sai

suka ce wallahi baban Abdurrahman babu abin da muke nufi

sai alheri. Sai ya ce ai da yawa mai son alheri ba zai taba

samun sa ba. Lalle Manzon Allah mai tsira da amincin Allah

ya gaya mana cewa akwai wasu mutane da za su rika karanta

Alkur’ani amma kuma ba zai wuce makogoronsu ba, Ina

rantsuwa da Allah watakila mafi yawansu daga cikinku suke.

Daga nan sai ya juya ya bar su)).

Intaha. Da kuma dogara

kan maganar babban Taabi’ii Hasanul Basarii wacce ta zo

cikin littafin Ibnu Wadh’dhah, da littafin Alitisam na

Shaatibii 1/111 inda ya ce: ((Mai yin bidi’ah ba zai Kara

kokari cikin azuminsa na bidi’ah ba, ko sallarsa ta bidi’ah

ba, face hakan ya nisantar da shi daga Allah)).

Dogara kan wadannan ayoyi da hadithai da maganganun

Sahabbai da Taabi’ai da kuka ji su yanzu ne ya sa muke

gargadin Al’ummar Musulmi, muke hana su rikon ranar

haihuwar Manzon Allah Mai tsira da amincin Allah a matsayin

ranar Idi, muke musu gargadin rikon bukin maulidi a matsayin

wani abu na addini da ake neman lada da shi a wurin Allah

Madaukakin Sarki!

Saboda abu ne tabbatacce wurin Maluman Musulunci cewa

Annabi Mai tsira da amincin Allah bai yi bukin maulidi ba,

Sahabbai ba su yi bukin maulidi ba, Taabi’ai ba su yi bukin

maulidi ba, Taabi’ut Taabi’in ba su yi bukin maulidi ba.

Duk kuwa abin da ba zama addini ba a zamanin Sahabbai, da

Taabi’ai, da Taabi’ut Taabi’in tare da kasancewar sababin

yin sa a lokacin nasu’ da kuma ikon yin sa daga gare su

yana nan’ amma kuma babu Wanda ya yi shi daga cikinsu,

to lalle wannan abin babu ta yadda za a yi ya zamanto

addini karbabbe a wurin na bayansu har zuwa tashin Kiyama.

Yan’uwa Musulmi! Lalle shi rikon ranar maulidi a matsayin

Idi, da maida shi ranar buki, ba a fara yin shi ba cikin

wannan Al’umma sai cikin karni na hudu na hijirar Annabi

Mai tsira da amincin Allah’ watau sai a cikin shekara ta

dari uku da settin da biyu (362). Sannan mutumin da ya fara

yin wannan buki na maulidi shi ne wani sarki dan Shi’ah

Fadimiyyah Mai suna Almu’izzu li Dininl Lah a garin

Alkahira’ kamar yadda yake rubuce cikin littattafan Musulunci

da tarihi, da wasunsu, kuna iya duba wadannan littattafan:-

ﺍﻟﻤﻮﺍﻋﻆ ﻭﺍﻻﻋﺘﺒﺎﺭ ﺑﺬﻛﺮ ﺍﻟﺨﻄﻂ ﻭﺍﻻﺛﺎﺭ ﻟﻠﻤﻘﺮﻳﺰﻱ ١ / ٤٩٠، ﻭﺻﺒﺢ

ﺍﻷﻋﺸﻰ ﻓﻲ ﺻﻨﺎﻋﺔ ﺍﻹﻧﺸﺎﺀ ﻟﻠﻘﻠﻘﺸﻨﺪﻱ ٣ / ٤٩٨، ﻭﺗﺎﺭﻳﺦ ﺍﻻﺣﺘﻔﺎﻝ

ﺑﺎﻟﻤﻮﻟﺪ ﺍﻟﻨﺒﻮﻱ ﻟﻠﺴﻨﺪﻭﺑﻲ ﺹ٦٩، ﻭﺃﺣﺴﻦ ﺍﻟﻜﻼﻡ ﻓﻴﻤﺎ ﻳﺘﻌﻠﻖ ﺑﺎﻟﺴﻨﺔ

ﻭﺍﻟﺒﺪﻋﺔ ﻣﻦ ﺍﻷﺣﻜﺎﻡ ﻟﻤﺤﻤﺪ ﺑﺨﻴﺖ ﺹ٤٤، ٤٥، ﻭﺍﻟﻤﺤﺎﺿﺮﺍﺕ ﺍﻟﻔﻜﺮﻳﺔ

ﻟﻠﺸﻴﺦ ﻋﻠﻲ ﻓﻜﺮﻱ ﺹ٨٤، ﻭﺍﻹﺑﺪﺍﻉ ﻓﻲ ﻣﻀﺎﺭ ﺍﻻﺑﺘﺪﺍﻉ ﻟﻠﺸﻴﺦ ﻋﻠﻲ

ﻣﺤﻔﻮﻅ ﺹ١٢٦، ﻭﺍﻟﺘﺎﺭﻳﺦ ﺍﻟﻌﺒﺎﺳﻲ ﻭﺍﻟﻔﺎﻃﻤﻲ ﻟﻠﺸﻴﺦ ﺍﺣﻤﺪ ﻣﺨﺘﺎﺭ ﺍﻟﻌﺒﺎﺩﻱ

ﺹ٢٦١، ٢٦٢ .

Almawaa’izu wa Litibaar na Maqriizii 1/490, da Subhul

A’ashaa na Qalqashandii 3/498, da Taariikhu Lihtifaali Bil

Maulidin Nabawii na Sanduubii shafi na 69, da Ahsanul Kalam

fi ma yataallaqu bis Sunnati wal Bidi’ati minal Ahkam na

Muhammad Bakhiit shafi na 44,45, da Almuhadharaatul

Fikriyyah na Ali Fikrii shafi na 84, da Al’ibdaa fi Madharri

Libtidaa na Ali Mahfuuz shafi na 126, da Taarikhul Abbaasii

wal Faatimii na Ahmad Mukhtaar Al’abbadii shafi na

261,262.

_#DR,JALO JALINGO_

Continue reading...

Wa’azin Sheikh Jafar Mahmoud Adam Na Karshe a Duniya Kuma Ga Matasa Da ‘Yan Siyasa

<b>Wa’azin Sheikh Jafar Mahmoud Adam Na Karshe a Duniya Kuma Ga Matasa Da ‘Yan Siyasa</b>

Wannan Nasihar Marigayi Sheikh Jafar Mahmoud Adam Rahimahullah ya gabatar da ita ne a ranar Alhamis 25 ga Rabi’ul Auwal, 1428. wato dai-dai da 12th April, 2007. Ya gabatar da wannan Nasihar a daren Juma’ar da aka kashe shi, a wajen muhadarar da aka shirya a masallacin Juma’a na Usman Bin Affan dake kofar Gadon kaya

. Bayan dawowar sa daga garin Bauchi.

Ita wannan muhadarar malamai uku ne suka gabatar da ita daga cikin su akwai sheikh Dr Muhammad Sani Umar R/lemu da Malam Muhammad Aminu Ibrahim Daurawa da sheikh Muhammad Nazeefi Inuwa. Wadannan sune malaman da suka gabatar da wannan muhadar, amma kasan cewar sheikh Jafar ya dawo daga tafiya ne sai aka bashi minti goma yayi ta’aliki. Ga kuma yadda ta’alikin nasa ya kasance :

Bayan Mallam ya yi godiya ga Allah, tare da yin salati ga manzon Allah salallahu alaihi wasallam, sannan ya yace “ya yan uwa musulmi abin da zan fada a nasiha ta ta karshe ’’ Allahu akbar wato wannan jumla ita Mallam ya fara bude maganarsa da ita, kamar yasan cewa washe gari juma’a zai riga mu gidan gaskiya, sai yaci gaba da cewa “Muji tsoran Allah, mu duka, muda zamuyi zabe’’ wato ya yi wannan Nasihar ne ana jajiberin tsamiya na zaben gwamnoni da na ‘yan majalisar jihohi, Sannan ya ci gaba da cewa “ muda zamuyi zabe da kuma wadan da za’a zaba.

Asalin zaben nan malamai sunyi bayanin sa. Dukkan mutumin da zaka zaba, to ya zama cewa zaka zabe shi ne ba don maslahar ka ba kai kadai, sai don maslahar al’umma gaba daya. Akwai mutanen da suke fama da kuncin tunani, wadan da su tunanin su me zasu samu a karkashin dan takara, sannan su ce a zabe shi; ko kuma me suka rasa suce kada a zabe shi. Inda dan takara zai zo yabani naira miliyan goma ni kadai a matsayi na na Ja’afar amma ya ha’inci alummar da yake wa mulki ta hanyar sauran bukatunsu, wadan da a asusun gwamnati akwai kudaden da za’a iya wadan nan bukatu amma yaki yi, Ni kuma in kalli miliyan goman nan ince ku zabe shi. To hakika na ci amanar kaina, kuma na ci amanar ku talakawa bayin Allah, shi kuma shugaba na haince shi. Inda shugaba zai hana ni ko kwabo, amma ya zanto kudaden daya karba daga asusun gwamnatin tarayya ya aiwatar da su ta hanyar da ta dace. To wajibi na ne, in kiraye ku cewa ku zabe shi. Ba a dauki ma’aunin na ni me na samu ko me na rasa ba, masu irin wannan sune wadan da suka jahilci Addini kuma suka jahilci rayuwa. Domin wannan shi ne yakai Nigeria cikin halin ka-ka-ni-ka-yi. Ganin in amfana ni kadai ko kuma a bude mana wata kafa mu yan tsiraru shi ke nan sai muyi shiru alhali mun san abin da shugaba yake yi ha’inci ne,amma sai mu daure masa gindi,hasali ma mu dinga kuruta jama’a cewa dole ne su zabe shi, ba don komai ba sai don abin da bai taka kara ya karya ba.

To wannan kuntataccen tunani ne, kuma rashin hangen nesa ne rashin sanin ya kamata ne. Kullum zaka kalli me muka samu na ci gaba, ba me ni kadai na samu ba ’’ Allahu akbar sai malam ya kara da cewa “ ina kira ga ku matasa ku lura da yadda ake amfani da ku ’’malam ya buga wani misalin abin da ya gani yayin da yake dawowa daga tafiya sai yace “ Da zu na shigo kano dab da lokacin sallar maghriba kafin zuwana nan sai naga wadan da suke kanfen (campaign) wato da alamu anyi yawo da su cikin garine za su koma gida. Naga yara matasa an ciko su akan akorukura su kusan hamsin acikin motar nan kai da ganin su babu wanda ya yi sallar azahar ballan tana la’asa kuma galibin su da alamun sun bugu mota tana ta layi dasu suna ihu suna dauke da hotuna suna sai wane sai wane kuma su wadan da suke bada kudi ayi hakan ciki babu ‘ya ‘yan su, nasu suna can, sun kai ‘ya ‘yan su mayan makarantu na cikin gida ko na waje. Wannan shi ne hakikanin cin amanar al-umma, kai wannan shi ne kakikanin rashin mutunci, ka haukata ya yan talakawa bayan ka yinwatar da su ka kuma ka jahiltar da su babu ilmin addini babu na rayuwa su kashe lokaci mai tsaho suna dauke da hotunan ka kan kana son ka tsaya zabe a wani mataki na zabe. Akan abin da za’a basu wanda bai gaza Naira dari uku ko da hamsin ba.

Sannan mallam ya cigaba da nanata maganar sa ta farko inda yace “Hakika wannan ya kamata ayi hattara, duk wanda zamu zaba, kada mu kalli me ya bamu, mu kalli dacewar sa da cancantar sa. Duk wanda zamu zaba ya kasance ya cancanta ko yabamu kudi ko bai bamu ba. Duk wanda bai cancanta ba to ko yabamu fan taba sama to mu kadashi wannan shi ne gaskiyar lamari, amma idan ku ka tsaya da jahilci da kuntatacciyar kwakwalwa ta ni an bani kaza ni naci kaza. To wannan tunani na ci bayane ba tunani ne na wanda yasan abin daya kamata ba’’.

Sai malam ya kara da cewa “Abin haushi da takaici hatta wadan su masu Magana da yawun Addini akwai masu irin wannan kuntataccen tunani ubangiji ta’ala ya yi mana gamdakatar’’.

Allahu akbar wannan it ace Nasihar da malam ya yi ta karshe ga matasa kai dama dukkan wani mutum mai hankali. Bayan an kammala wannan muhadarar da niyyar washe gari juma’a malam zai yi khudba akan zabe. Ranar juma’a da asubahi malam yana cikin sallah,ya karanta suratul Ma’arij aka samu wasu mutane miyagu azzalumai makiya Allah makiya san cigaban Addini, suka yi masa harbi da bindiga ba sau daya ba, ba sau biyu ba, kisan gilla inda suka harbe shi a kirjinsa na gefen hagu.

Anan muna rokon Allah ta’ala ya sa malam ya yi mutuwar shahada kuma ya karbi shahadar sa, Allah ya kyautata bayansa, ya sanya Albarka a cikin iyalansa da zurriyarsa. wadanda suka aikata wannan aiki na ta'addanci a’ansa, su sani wannan tafarki da Mallam Jafar ya mutu akansa, kamar wata bishiya ce da bata tsiro bata tofo har sai mun shayar da ita da jinin jikinmu, wannan abu ko kadan bazai sanyamu mu yi rauni ba akan wannan tafarki. Allah ya daukaka Musulunci da Musulmai, ya Allah kada ka baiwa azzalumai dama domin su cutar da al’umma.

Continue reading...

LAFAZIN MARGAYI SHEIKH JA'AFAR MAHMUD ADAM (R) GAME DA MAULUDI

LAFAZIN MARGAYI SHEIKH
JA'AFAR MAHMUD ADAM (R)
GAME DA MAULUDI
.
Malam yaci gaba da cewa:
.
"Shi yasa lokacin da muke musu da
wadansu yan uwa kan batun
MAULIDI MAULIDI MAULIDI
muka ce duk abune mai sauqi da
AKHADAREE da ISHIMAWEE da
IZIYYAH da RISALA da ASKAREE
da MUKHUTASAR, wadannan duk
littattafai ne na koyon addini da mu
da ku duk muna koyon addini a
cikin su amma babu daya daga
cikin su da ya kawo BABI KO
FASALI NA MAULIDI.
.
Yanzu muna neman illa da tasa
basu kawo ba, shin sun yi mantuwa
ne? Sun jahilta ne? Ko ko ba addini
ba ne don haka ba su kawo ba???
.
Saboda haka cikin wadannan dole
ayi daya ko dai ya kasance
mantuwa sukayi? ko ko ilimin su ne
bai kai ba? Koko a fahimtar su shi
din ba addini ba ne? Shiyasa basu
kawo shi ba?"
.
Mallam har ya rasu baku kawo
masa wadannan amsoshin ba, to
mu har yanzu muna jira ku kawo
mana, idan har kun gagara kawowa
to muna kiran ku da kuji tsoron
Allah ku dawo kubi karantarwar
Alqur'ani da Sunnar Annabi (saw)
sai ku samu hutu a rayuwar ku ta
duniya da lahira.
.
YA ALLAH KA JIQAN SHEIKYA ALLAH KA JIQAN
SHEIKH Ja'afar.

Continue reading...

MUSABAKAR HADDAR ALQUR’ANI KO HADITHI KO WANI NAU’IN ILMI A MAHANGAR MUSULUNCI(Dr. Ibrahim Jalo Jalingo)



Da yawa daga cikin wadanda suka zaba wa kansu
sabanin shiriyar Manzon Allah cikin gudanar da
addininsu suna ganin cewa: In har Idin Maulidi
bidi’ah ne, to kuwa lalle Musabaka a kan haddar
Alqur’ani Mai girma, ko haddar Hadithan Annabi
masu daraja ko haddar wani ilmi na Musulunci su
ma yin su bidi’ah ce!!!
*************************

A nan muna ganin cewa yawan nisantar wadannan
mutane ga littattafan Shari’ah na maluman
Musulunci ne ya sa ba su ma san cewa: Dukkan
abin da halaccinsa ya tabbata ta yanyar Ijma’in
Musulmi cikin wani zamani daga cikin zamuna, to
dole ne ya zamanto daya daga cikin abubuwa uku:-
1- ko dai ya zamanto Mubaahi, watau abin da yin
sa da rashin yin sa duk daya a idanun Shari’ah.
2- ko kuwa ya zamanto Mustahabbi, watau abin da
in har ba a yi shi ba to ba a yi wani laifi ba, in
kuma aka yi shi to ana da wani lada na
musamman.
3- ko kuwa ya zamanto Waajibi, watau abin da in
har ba a yi shi ba za a sami zunubi, in kuma an yi
shi to an yi abin da Shari’ah ta tilasta yin shi.
******************************

shi kuwa Musabaka domin haddar Alqur’ani Mai
girma abu ne da Maluman Sunnah, da su kansu
masu bidi’ah na Duniya suka hadu a kan halaccinsa
a bisa hujjar kiyasin shi a kan Musaabakokin da
Nassi ya zo da halaccinsu. In kuwa haka lamarin
yake, to ta kaka ne za a hada hukuncin Musaabaka
domin haddar Alqur’ani da hukuncin Idin Maulidin
da babu mai yin shi ko halatta shi in banda wasu
daga cikin masu yin bidi’ah??
*********************

HUKUNCIN MUSABAKA:
1. Imam Ibnu Qudaamah mai rasuwa a shekara ta
620 watau da mutuwarsa yau shekaru 815 ke nan,
ya ce cikin littafinsa mai suna Almugnii
13/404-405 :-
{ ﻟﻤﺴﺎﺑﻘﺔ ﺟﺎﺋﺰﺓ ﺑﺎﻟﺴﻨﺔ ﻭﺍﻻﺟﻤﺎﻉ، ﺍﻣﺎ ﺍﻟﺴﻨﺔ ﻓﺮﻭﻯ ﺍﺑﻦ ﻋﻤﺮ ﺍﻥ
ﺍﻟﻨﺒﻲ ﺻﻠﻰ ﺍﻟﻠﻪ ﻋﻠﻴﻪ ﻭﺳﻠﻢ ﺳﺎﺑﻖ ﺑﻴﻦ ﺍﻟﺨﻴﻞ ﺍﻟﻤﻀﻤﺮﺓ ﻣﻦ ﺍﻟﺤﻔﻴﺎﺀ
ﺍﻟﻰ ﺛﻨﻴﺔ ﺍﻟﻮﺩﺍﻉ، ﻭﺑﻴﻦ ﺍﻟﺘﻲ ﻟﻢ ﺗﻀﻤﺮ ﻣﻦ ﺛﻨﻴﺔ ﺍﻟﻮﺩﺍﻉ ﺍﻟﻰ ﻣﺴﺠﺪ
ﺑﻨﻲ ﺯﺭﻳﻖ . ﻣﺘﻔﻖ ﻋﻠﻴﻪ … ﻭﺍﺟﻤﻊ ﺍﻟﻤﺴﻠﻤﻮﻥ ﻋﻠﻰ ﺟﻮﺍﺯ ﺍﻟﻤﺴﺎﺑﻘﺔ ﻓﻲ
ﺍﻟﺠﻤﻠﺔ . ﻭﺍﻟﻤﺴﺎﺑﻘﺔ ﻋﻠﻰ ﺿﺮﺑﻴﻦ : ﻣﺴﺎﺑﻘﺔ ﺑﻐﻴﺮ ﻋﻮﺽ، ﻭﻣﺴﺎﺑﻘﺔ
ﺑﻌﻮﺽ . ﻓﺎﻟﻤﺴﺎﺑﻘﺔ ﺑﻐﻴﺮ ﻋﻮﺽ ﻓﺘﺠﻮﺯ ﻣﻄﻠﻘﺎ ﻣﻦ ﻏﻴﺮ ﺗﻘﻴﻴﺪ ﺑﺸﻲﺀ
ﻣﻌﻴﻦ، ﻛﺎﻟﻤﺴﺎﺑﻘﺔ ﻋﻠﻰ ﺍﻻﻗﺪﺍﻡ، ﻭﺍﻟﺴﻔﻦ، ﻭﺍﻟﻄﻴﻮﺭ، ﻭﺍﻟﺒﻐﺎﻝ، ﻭﺍﻟﺤﻤﺮ،
ﻭﺍﻟﻤﺰﺍﺭﻳﻖ، ﻭﺍﻟﻤﺼﺎﺭﻋﺔ، ﻭﺭﻓﻊ ﺍﻟﺤﺠﺮ ﻟﻴﻌﺮﻑ ﺍﻻﺷﺪ، ﻭﻏﻴﺮ ﺫﻟﻚ؛ ﻻﻥ
ﺍﻟﻨﺒﻲ ﺻﻠﻰ ﺍﻟﻠﻪ ﻋﻠﻴﻪ ﻭﺳﻠﻢ ﻛﺎﻥ ﻓﻲ ﺳﻔﺮ ﻣﻊ ﻋﺎﺋﺸﺔ ﻓﺴﺎﺑﻘﺘﻪ ﻋﻠﻰ
ﺭﺟﻠﻬﺎ، ﻓﺴﺒﻘﺘﻪ، ﻗﺎﻟﺖ : ﻓﻠﻤﺎ ﺣﻤﻠﺖ ﺍﻟﻠﺤﻢ ﺳﺎﺑﻘﺘﻪ ﻓﺴﺒﻘﻨﻲ، ﻓﻘﺎﻝ :
ﻫﺬﻩ ﺑﺘﻠﻚ . ﺭﻭﺍﻩ ﺍﺑﻮﺩﺍﻭﺩ . ﻭﺳﺎﺑﻖ ﺳﻠﻤﺔ ﺑﻦ ﺍﻻﻛﻮﻉ ﺭﺟﻼ ﻣﻦ ﺍﻻﻧﺼﺎﺭ
ﺑﻴﻦ ﻳﺪﻱ ﺍﻟﻨﺒﻲ ﺻﻠﻰ ﺍﻟﻠﻪ ﻋﻠﻴﻪ ﻭﺳﻠﻢ ﻓﻲ ﻳﻮﻡ ﺫﻱ ﻗﺮﺩ . ﻭﺻﺎﺭﻉ
ﺍﻟﻨﺒﻲ ﺻﻠﻰ ﺍﻟﻠﻪ ﻋﻠﻴﻪ ﻭﺳﻠﻢ ﺭﻛﺎﻧﺔ ﻓﺼﺮﻋﻪ . ﺭﻭﺍﻩ ﺍﻟﺘﺮﻣﺬﻱ . ﻭﻣﺮ
ﺑﻘﻮﻡ ﻳﺮﺑﻌﻮﻥ ﺣﺠﺮﺍ ﻳﻌﻨﻲ ﻳﺮﻓﻌﻮﻧﻪ ﻟﻴﻌﺮﻓﻮﺍ ﺍﻻﺷﺪ ﻣﻨﻬﻢ ﻓﻠﻢ ﻳﻨﻜﺮ
ﻋﻠﻴﻬﻢ . ﻭﺳﺎﺋﺮ ﺍﻟﻤﺴﺎﺑﻘﺎﺕ ﻳﻘﺎﺱ ﻋﻠﻰ ﻫﺬﺍ .{ ﺍﻧﺘﻬﻰ .
Ma’ana: ((Musabaka halal ce cikin sunnar Manzon
Allah, da Ijma’in Maluma. A cikin Sunnah dai Ibnu
Umar ya ruwaito cewa Annabi mai tsira da amincin
Allah ya shirya Musabaka tsakanin dawakin da aka
yi musu “Tadhmiir” (watau wadanda aka yi musu
horon tinkarar yaki ta hanyar karanta abinci gare su
da sanya musu tufafinsu da sauransu) a filin da ya
taso daga Haifaa har zuwa Thaniyyatul Wadaa, haka
nan ya shirya wata Musabakar tsakanin dawakin da
ba a yi musu Tadhmiiri ba, a filin da ya taso daga
Thaniyyatul Wadaa har zuwa Masjidu Bani Zuraiq.
Buhari da Muslim ne suka ruwaito hadithin…Sannan
Musulmi sun yi Ijma’i a kan halaccin Musabaka a
dunkule. Sannan ita Musabaka ta kasu ne zuwa
kashi biyu: Musabaka da ake yi tare da sanya wasu
kudi cikinta (ga duk wanda ya yi nasara). Akwai
kuma Musabaka da ake yi ba tare da an sanya kudi
cikinta (ga duk wanda ya yi nasara ba). To ita
Musabaka da ake yi ba tare da an sanya wasu kudi
cikinta ba wannan ta halatta ba tare da sanya mata
wani tarnaki a cikinta ba, kamar dai Musabakar da
ake yi na tseren gudu da kafa, ko Musabakar tseren
jiragen ruwa, ko Musabakar tsere tsakanin tsutsaye,
ko Musabakar tsere tsakanin alfadaru, ko
Musabakar tsere tsakanin jakuna, ko Musabakar
tsere tsakanin giwaye, ko Musabakar yin harbi da
kananan masu, ko Musabakar yin kokowa, ko
Musabakar daga dutse mai nauyi sanoda gwada
karfi, da dai nau’o’in Musabaka dabam daban.
Saboda Annbi mai tsira da amincin Allah wata rana
a hanyar tafiye-tafiyensa ya yi Musabakar tseren
gudu da kafa tsakaninsa da matarsa Nana A’isha
Allah Ya kara mata yarda, kuma ta yi nasara a
kansa. Sai A’isha ta ce: da na yi kiba sai wata rana
muka sake yin Musabakar tseren gudu da kafa sai
ya yi nasara a kaina. Sai ya ce da ni: ni ma na rama
wancan ci da kika yi mini. Wannan hadithi Abu
Dawuda ne ya ruwaito shi. Kuma Salamah Dan
Ak’wa ya yi Musabakar tsere da kafa tsakaninsa da
wani mutum a gaban Annabi mai tsira da amincin
Allah a ranar Ruwan Zuu Qarad. Sannan Annabi mai
tsira da amincin Allah ya yi Musabakar kokowa
tsakaninsa da wani gwanin kokowa mai suna
Rukaanah, kuma ya yi nasara a kansa ya kada shi.
Tirmizii ne ya ruwaito hafithin. Sannan wata rana
Annabi mai tsira da amincin Allah ya wuce wasu
mutane suna Musabakar daga dutse mai nauyi
saboda sanin wane ne ya fi karfi, amma bai hana su
yin hakan ba. Sauran Musabakpkin sai a kiyasta su
a kan wadannan)) [da nassi ya tabbatar]. Intaha.
2. Imamu Ibnu Qayyimil Jauziyyah wanda ya mutu a
shekarar Hijira ta 751 watau yau shekaru 684 ke
nan da suka wuce ya ce cikin littafinsa mai suna
Alfuruusiyyah 1/318:-
{ ﺍﻟﻤﺴﺎﻟﺔ ﺍﻟﺤﺎﺩﻳﺔ ﻋﺸﺮﺓ : ﺍﻟﻤﺴﺎﺑﻘﺔ ﻋﻠﻰ ﺣﻔﻆ ﺍﻟﻘﺮﺍﻥ، ﻭﺍﻟﺤﺪﻳﺚ،
ﻭﺍﻟﻔﻘﻪ، ﻭﻏﻴﺮﻩ ﻣﻦ ﺍﻟﻌﻠﻮﻡ ﺍﻟﻨﺎﻓﻌﺔ، ﻭﺍﻻﺻﺎﺑﺔ ﻓﻲ ﺍﻟﻤﺴﺎﺋﻞ، ﻫﻞ ﺗﺠﻮﺯ
ﺑﻌﻮﺽ؟ ﻣﻨﻌﻪ ﺍﺻﺤﺎﺏ ﻣﺎﻟﻚ، ﻭﺍﺣﻤﺪ، ﻭﺍﻟﺸﺎﻓﻌﻲ . ﻭﺟﻮﺯﻩ ﺍﺻﺤﺎﺏ
ﺍﺑﻲ ﺣﻨﻴﻔﺔ، ﻭﺷﻴﺨﻨﺎ، ﻭﺣﻜﺎﻩ ﺍﺑﻦ ﻋﺒﺪ ﺍﻟﺒﺮ ﻋﻦ ﺍﻟﺸﺎﻓﻌﻲ . ﻭﻫﻮ ﺍﻭﻟﻰ
ﻣﻦ ﺍﻟﺸﺒﺎﻙ، ﻭﺍﻟﺼﺮﺍﻉ، ﻭﺍﻟﺴﺒﺎﺣﺔ، ﻓﻤﻦ ﺟﻮﺯ ﺍﻟﻤﺴﺎﺑﻘﺔ ﻋﻠﻴﻬﺎ ﺑﻌﻮﺽ،
ﻓﺎﻟﻤﺴﺎﺑﻘﺔ ﻋﻠﻰ ﺍﻟﻌﻠﻢ ﺍﻭﻟﻰ ﺑﺎﻟﺠﻮﺍﺯ، ﻭﻫﻲ ﺻﻮﺭﺓ ﻣﺮﺍﻫﻨﺔ ﺍﻟﺼﺪﻳﻖ
ﻟﻜﻔﺎﺭ ﻗﺮﻳﺶ ﻋﻠﻰ ﺻﺤﺔ ﻣﺎ ﺍﺧﺒﺮﻫﻢ ﺑﻪ، ﻭﺛﺒﻮﺗﻪ . ﻭﻗﺪ ﺗﻘﺪﻡ ﺍﻧﻪ ﻟﻢ
ﻳﻘﻢ ﺩﻟﻴﻞ ﺷﺮﻋﻲ ﻋﻠﻰ ﻧﺴﺨﻪ . ﻭﺍﻥ ﺍﻟﺼﺪﻳﻖ ﺍﺧﺬ ﺭﻫﻨﻬﻢ ﺑﻌﺪ ﺗﺤﺮﻳﻢ
ﺍﻟﻘﻤﺎﺭ . ﻭﺍﻥ ﺍﻟﺪﻳﻦ ﻗﻴﺎﻣﻪ ﺑﺎﻟﺤﺠﺔ، ﻭﺍﻟﺠﻬﺎﺩ، ﻓﺎﺫﺍ ﺟﺎﺯﺕ ﺍﻟﻤﺮﺍﻫﻨﺔ
ﻋﻠﻰ ﺍﻻﺕ ﺍﻟﺠﻬﺎﺩ، ﻓﻬﻲ ﻓﻲ ﺍﻟﻌﻠﻢ ﺍﻭﻟﻰ ﺑﺎﻟﺠﻮﺍﺯ . ﻭﻫﺬﺍ ﺍﻟﻘﻮﻝ ﻫﻮ
ﺍﻟﺮﺍﺟﺢ .{ ﺍﻧﺘﻬﻰ .
Ma’ana: ((Mas’alah ta goma sha daya: Yin
Musabakar haddace Alkur’ani, da Hadithi, da Fiqhu,
da wasu Ilmummuka masu amfani, ko gane abin da
yake daidai cikin wasu mas’alolin, shirya irin
wannan Musabaka a bisa wani kudi, shin hakan zai
halatta ko kuwa ba zai halatta ba? Mutanen Malik,
da Ahmad, da Sha’fi’ii sun hana yin sa. Amma
mutanen Abu Hanifah da Malaminmu (Ibnu
Taimiyah) da ma hikayar Ibnu Abdil Barr daga
Sha’fi’ii sun halatta yinsa. Shi wannan nau’i na
Musabaka ya fi yin Musabaka a kan harkar iya sa
tarko, ko kokowa, ko ninkaya, sanoda haka
wadanda suka halatta shirya Musabaka a bisa kudi
cikin wadannan, lalle shirya Musabaka cikin harkokin
habaka ilmi shi zai fi cancantar halatta, kuma
wannan ita ce surar Muraahanar da Sbubakar Siddiq
ya yi da kafuran Quraishawa a kan gaskiyar labarin
da ya ba su (na cewa Ruumaawa za su yi nasara a
kan Faatisaawa bayan shekaru kadan). Dalili ya
gabata na cewa babu abin da ya shafe ingancin
wannan Muraahanar. Kuma shi Abubakar ya yi
Muraahanar da su ne bayan haramta yin caca.
Sannan ita tsayuwar Addini da ma tana samuwa ne
ta hanyar kafa hujja, da yin jihadi, saboda wannan
idan har Muraahanah za ta halatta a kan abubuwan
karfafa jihadi, ke nan ta halatta a kan abubuwan
karfafa ilmi da za su karfafa kafa hujja shi ne zai fi
cancanta, kuma wannan magana ita ce abin
rinjayarwa)). Intaha.
******************************
Lalle da wadannan bayanai ne mahankalta za su
fahimci cewa ita Musabakar haddar Alkur’ani mai
girma, ko musabakar haddar Hadithan Manzon Allah
Masu daraja, ko musabakar haddar wani ilmi mai
amfani -tare da sanya wani kudi ga wanda ya yi
nasara ko kuwa ba tare da sanya wani kudi ga
wanda ya yi nasara ba- abu ne da yake halal ta
hanyar hujjoji biyu:-
1. Ijma’i.
2. Qiyaasi.
Wannan kuwa duka sabanin maida ranar haihuwar
Annabi mai tsira da amincin Allah wani Idi ne,
wanda babu Ijma’i a kansa, babu kuma wani
Qiyaasi sahihi a kansa. Muna rokon Allah Ya
taimake mu Ya tabbatar da dugaduganmu a kan
Sunnar Annabi mai tsira da amincin Allah. Ameen.

Continue reading...
 

Random Posts

3/random/post-list
X

Contact Form

Name

Email *

Message *